A yau Litinin ne bankin samar da ci gaba na Sin, da bankin shige da fice na Afirka, suka sanya hannu kan yarjejeniyar samar da rancen kudi na musamman har dalar Amurka miliyan 400, domin tallafawa wajen bunkasa kanana da matsakaitan kamfanoni dake nahiyar Afirka.
An dai sanya hannu kan yarjejeniyar samar da kudaden rancen ne a birnin Alkahirar kasar Masar. Ana kuma sa ran yin amfani da kudaden lamunin wajen inganta yanayin samar da kudade ga kanana da matsakaitan kamfanonin dake Afirka, ta yadda za su samu zarafin cin gajiyar hidimomin kudi masu yalwa, cikin sauki da kyawawan ka’idoji. Kaza lika matakin zai ingiza bunkasar tattalin arziki, da cinikayya, da hadin gwiwar hada hadar kudade tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp