• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma

by CMG Hausa
3 years ago
Hijira

‘Yan gudun hijira mutane ne mafi fama da mawuyacin hali a duniya. Idan dai akwai dama, to, ba za su yi watsi da gidajensu, da barin iyalai, har su fita zuwa wata kasa ta daban ba, inda suke jure zaman rayuwa cike da wahalhalu. Sai dai yanzu har ana kara wulakanta su: Kasar da suke kaura cikinta ka iya tusa keyarsu zuwa wani wuri mai nisa, inda ba su taba tunani ko tsammanin zuwa ba.

A ranar 14 ga wata, kotun kare hakkin dan Adam ta nahiyar Turai ta hana tashin wani jirgin sama mai daukar nauyin jigilar ‘yan gudun hijira daga kasar Birtaniya zuwa Rwanda.

  • Xi Ya Yi Kira A Hada Gwiwa Don Yaki Da Rashawa

Kafin afkuwar lamarin, kasar Birtaniya da Rwanda sun kulla wata yarjejeniya, inda aka daddale cewa, Birtaniya zata biya kudi fam miliyan 120 ga Rwanda, don kasar Rwandan ta karbi ‘yan gudun hijira da suka yi satar ketarawa zuwa kasar Birtaniya. Ko da yake, ba a fara gudanar da yarjejeniyar ba tukuna, sakamakon kin amincewar da bangarorin kasa da kasa suka nuna, ciki har da hukumar ‘yan gudun hijira ta MDD suka nuna. Amma gwamnatin kasar Birtaniya tana ci gaba da neman aiwatar da yarjejeniyar.

Me ya sa ake kin amincewa da matakin da kasar Birtaniya ta dauka?
Saboda da farko dai, kasar Birtaniya, da Amurka, da sauran kasashen yammacin duniya, laifinsu ne yadda suka haddasa matsalar samun tarin ‘yan gudun hijira a duniya. Wadannan kasashe sun kaddamar da yake-yake a kasashen Iraki, da Afghanistan, da tsoma baki tare da tsananta yanayin rikici a Syria, da Libya, da Venezuela, da dai sauransu.

Hijira

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

Irin matakan da suka dauka sune ainihin dalilan da suka haddasa karuwar ‘yan gudun hijira a duniya. Saboda haka ya kamata kasashen yamma su dauki nauyin kula da ‘yan gudun hijira, maimakon a tusa keyarsu zuwa wata kasar dake nahiyar Afirka.

Ban da wannan kuma, matakin kasar Birtaniya ya nuna wani yanayi na rashin adalci, inda matukar akwai kudi, to, ana iya yin kome. Su kasashe masu sukuni, sai su biya kudi, sa’an nan za su iya magance daukar nauyin kulawa da ‘yan gudun hijira.

Ganin haka zai sa su ta da rikici, da lalata yanayin zaman rayuwar jama’ar sauran kasashe, ba tare da wata damuwa ba. Idan an samu ‘yan gudun hijira, sai a tusa keyarsu zuwa kasashe masu tasowa, ba tare da tsoron samun wani tasiri daga lamarin ba.

Sa’an nan lamarin ya nuna halayyar kasashen yamma a fannin hakkin dan Adam. Da ma kasashen suna kallon kansu a matsayin “Masu kare hakkin dan Adam a duniya”, har ma su kan tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashe.

Sai dai ko da gaske ne suna kare hakkin dan Adam a duniya? Idan mun dauki kasashen Amurka da Birtaniya a matsayin misali. Kasar Amurka ta yi ta kaddamar da yake-yake a kasashe da dama, inda take kisan mutanen kasashen, da aiwatar da mulkin danniya a duniya. Yayin da a nata bangare, kasar Birtaniya tana kallon ‘yan gudun hijira a matsayin kayayyaki, tana neman mika su ga sauran kasashe ba tare da kulawa da yanayin da wadannan mutane suke ciki ba.

Ta wadannan batutuwa, za mu iya ganin cewa, kasashen yamma kullum suna neman sanya sauran kasashe kulawa da hakkin dan Adam, maimakon su da kansu su yi haka.

Batun nan ya shaida gaskiyar wata tsohuwar magana dake cewa: “A yi bincike kan halayyar wani mutum bisa aikace-aikacensa, maimakon kalmomin da ya fada”. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.