• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan gudun hijira mutane ne mafi fama da mawuyacin hali a duniya. Idan dai akwai dama, to, ba za su yi watsi da gidajensu, da barin iyalai, har su fita zuwa wata kasa ta daban ba, inda suke jure zaman rayuwa cike da wahalhalu. Sai dai yanzu har ana kara wulakanta su: Kasar da suke kaura cikinta ka iya tusa keyarsu zuwa wani wuri mai nisa, inda ba su taba tunani ko tsammanin zuwa ba.

A ranar 14 ga wata, kotun kare hakkin dan Adam ta nahiyar Turai ta hana tashin wani jirgin sama mai daukar nauyin jigilar ‘yan gudun hijira daga kasar Birtaniya zuwa Rwanda.

  • Xi Ya Yi Kira A Hada Gwiwa Don Yaki Da Rashawa

Kafin afkuwar lamarin, kasar Birtaniya da Rwanda sun kulla wata yarjejeniya, inda aka daddale cewa, Birtaniya zata biya kudi fam miliyan 120 ga Rwanda, don kasar Rwandan ta karbi ‘yan gudun hijira da suka yi satar ketarawa zuwa kasar Birtaniya. Ko da yake, ba a fara gudanar da yarjejeniyar ba tukuna, sakamakon kin amincewar da bangarorin kasa da kasa suka nuna, ciki har da hukumar ‘yan gudun hijira ta MDD suka nuna. Amma gwamnatin kasar Birtaniya tana ci gaba da neman aiwatar da yarjejeniyar.

Me ya sa ake kin amincewa da matakin da kasar Birtaniya ta dauka?
Saboda da farko dai, kasar Birtaniya, da Amurka, da sauran kasashen yammacin duniya, laifinsu ne yadda suka haddasa matsalar samun tarin ‘yan gudun hijira a duniya. Wadannan kasashe sun kaddamar da yake-yake a kasashen Iraki, da Afghanistan, da tsoma baki tare da tsananta yanayin rikici a Syria, da Libya, da Venezuela, da dai sauransu.

Hijira

Labarai Masu Nasaba

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Irin matakan da suka dauka sune ainihin dalilan da suka haddasa karuwar ‘yan gudun hijira a duniya. Saboda haka ya kamata kasashen yamma su dauki nauyin kula da ‘yan gudun hijira, maimakon a tusa keyarsu zuwa wata kasar dake nahiyar Afirka.

Ban da wannan kuma, matakin kasar Birtaniya ya nuna wani yanayi na rashin adalci, inda matukar akwai kudi, to, ana iya yin kome. Su kasashe masu sukuni, sai su biya kudi, sa’an nan za su iya magance daukar nauyin kulawa da ‘yan gudun hijira.

Ganin haka zai sa su ta da rikici, da lalata yanayin zaman rayuwar jama’ar sauran kasashe, ba tare da wata damuwa ba. Idan an samu ‘yan gudun hijira, sai a tusa keyarsu zuwa kasashe masu tasowa, ba tare da tsoron samun wani tasiri daga lamarin ba.

Sa’an nan lamarin ya nuna halayyar kasashen yamma a fannin hakkin dan Adam. Da ma kasashen suna kallon kansu a matsayin “Masu kare hakkin dan Adam a duniya”, har ma su kan tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashe.

Sai dai ko da gaske ne suna kare hakkin dan Adam a duniya? Idan mun dauki kasashen Amurka da Birtaniya a matsayin misali. Kasar Amurka ta yi ta kaddamar da yake-yake a kasashe da dama, inda take kisan mutanen kasashen, da aiwatar da mulkin danniya a duniya. Yayin da a nata bangare, kasar Birtaniya tana kallon ‘yan gudun hijira a matsayin kayayyaki, tana neman mika su ga sauran kasashe ba tare da kulawa da yanayin da wadannan mutane suke ciki ba.

Ta wadannan batutuwa, za mu iya ganin cewa, kasashen yamma kullum suna neman sanya sauran kasashe kulawa da hakkin dan Adam, maimakon su da kansu su yi haka.

Batun nan ya shaida gaskiyar wata tsohuwar magana dake cewa: “A yi bincike kan halayyar wani mutum bisa aikace-aikacensa, maimakon kalmomin da ya fada”. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester United Za Ta Mika Sabon Tayin Kudi Domin Sayan De Jong

Next Post

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

Related

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

4 hours ago
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

5 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

6 hours ago
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

7 hours ago
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
Daga Birnin Sin

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

8 hours ago
Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana

9 hours ago
Next Post
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.