• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Za Ta Gudanar Da Zaɓen Shugabannin Ƙananan Hukumomi A Watan Agusta

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Bauchi

Hukumar shirya zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi (BASIEC) ta shirya gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da suke jihar Bauchi ranar 10 ga watan Agustan 2024. 

Shugaban hukumar BASIEC, Ahmed Makama, shi ne ya sanar da hakan a hirarsa da manema labarai a ranar Juma’a, ya na mai bada tabbatar cewa hukumar ta shirya gudanar da sahihi, ingattaccen kuma karɓaɓɓen zaɓe ga kowani ɓangare.

  • Goron Juma’a
  • Yajin Aiki: NAHCON Ta Gargadi NLC Kan Janyo Cikas Ga Jigilar Maniyyata

Ya ce bisa yadda suke ƙunshe a dokoki, BASIEC ta samu umarnin gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi cikin kwanaki 60 masu zuwa.

A cewarsa, “Idan ku ka lissafi kwanaki 60 daga yau, zai kasance ranar 6 ga watan Agusta ne kuma ba ranar Asabar ba, sannan, yawancin lokuta an saba gudanar da zaɓuka a ranakun Asabar. Don haka mun tura zaɓen zuwa ranar 10 ga watan Agustan 2024.”

Ahmed Malama ya cigaba da cewa BASIEC za ta yi amfani da adadin masu rajistan zaɓe na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) wajen gudanar da zaɓen, yana mai cewa su a ɓangarensu ba su cika ajiye jerin masu rijistan zaɓe ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Shugaban hukumar zaɓen ya kuma sanar da cewa an fara sayar da fom ɗin neman tsayawa takara ga dukkanin mutanen da suke da buƙata da su fito su sayi fom ɗin.

Daga bisani sai shugaban ya yi ƙira ga jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki da su bi dokokin da aka gindaya wajen taimaka wa shirye-shiryen gudanar da zaɓen domin ganin an yi cikin kwanciyar hankali.

Ahmed ya tunatar da ‘yan siyasa da jam’iyyunsu cewa lokacin fara gangamin yaƙin neman zaɓe zai fara ne kwanaki 30 da lokacin gudanar da zaɓen kamar yadda yake ƙunshe cikin doka. Sai ya shawarci masu ruwa da tsaki da su yi biyayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.