• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Za Ta Gudanar Da Zaɓen Shugabannin Ƙananan Hukumomi A Watan Agusta

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Bauchi Za Ta Gudanar Da Zaɓen Shugabannin Ƙananan Hukumomi A Watan Agusta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shirya zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi (BASIEC) ta shirya gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da suke jihar Bauchi ranar 10 ga watan Agustan 2024. 

Shugaban hukumar BASIEC, Ahmed Makama, shi ne ya sanar da hakan a hirarsa da manema labarai a ranar Juma’a, ya na mai bada tabbatar cewa hukumar ta shirya gudanar da sahihi, ingattaccen kuma karɓaɓɓen zaɓe ga kowani ɓangare.

  • Goron Juma’a
  • Yajin Aiki: NAHCON Ta Gargadi NLC Kan Janyo Cikas Ga Jigilar Maniyyata

Ya ce bisa yadda suke ƙunshe a dokoki, BASIEC ta samu umarnin gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi cikin kwanaki 60 masu zuwa.

A cewarsa, “Idan ku ka lissafi kwanaki 60 daga yau, zai kasance ranar 6 ga watan Agusta ne kuma ba ranar Asabar ba, sannan, yawancin lokuta an saba gudanar da zaɓuka a ranakun Asabar. Don haka mun tura zaɓen zuwa ranar 10 ga watan Agustan 2024.”

Ahmed Malama ya cigaba da cewa BASIEC za ta yi amfani da adadin masu rajistan zaɓe na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) wajen gudanar da zaɓen, yana mai cewa su a ɓangarensu ba su cika ajiye jerin masu rijistan zaɓe ba.

Labarai Masu Nasaba

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Shugaban hukumar zaɓen ya kuma sanar da cewa an fara sayar da fom ɗin neman tsayawa takara ga dukkanin mutanen da suke da buƙata da su fito su sayi fom ɗin.

Daga bisani sai shugaban ya yi ƙira ga jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki da su bi dokokin da aka gindaya wajen taimaka wa shirye-shiryen gudanar da zaɓen domin ganin an yi cikin kwanciyar hankali.

Ahmed ya tunatar da ‘yan siyasa da jam’iyyunsu cewa lokacin fara gangamin yaƙin neman zaɓe zai fara ne kwanaki 30 da lokacin gudanar da zaɓen kamar yadda yake ƙunshe cikin doka. Sai ya shawarci masu ruwa da tsaki da su yi biyayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Pakistan Da Mataimakin Shugaban Kasar Brazil

Next Post

Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

Related

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

17 minutes ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

1 hour ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

3 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

4 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

5 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

5 hours ago
Next Post
Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

LABARAI MASU NASABA

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.