• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 hours ago
CIIE

Yanzu haka, bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin (CIIE) karo na 8 yana gudana a birnin Shanghai na Sin. A wajen bikin, Najeriya na daya daga cikin kasashen da suka samu matsayin Manyan Baki (Guests of Honor). Saboda haka, Najeriya ta tura wata babbar tawaga, a karkashin jagorancin shugaban majalisar wakilai ta kasar, Abbas Tajudeen, domin halartar bikin. Inda kuma ake shirin gudanar da wani taron tallata kayayyakin Najeriya na musamman.

 

A shafin yanar gizon bikin CIIE, an rubuta bayanin tallar Najeriya kamar haka: “Kamshin koko da na gyada, tamkar tsaraba ce daga kogin Kwara. Ruwan kogin na gudana ba tare da tsayawa ba, wanda ya taimaka wajen samar da dimbin amfanin gona. Najeriya, babbar bakuwa, na jiran ku a bikin CIIE karo na 8.” Bayanin nan ya nuna ni’imtaccen muhalli, da dimbin albarkatun noma na Najeriya.

 

Bikin CIIE shi ne bikin irinsa na farko da aka gudanar a duniya, wanda ya fi dora muhimmanci wajen baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su daga ketare. Kasar Sin ta kaddamar da bikin a shekarar 2018, da zummar aiwatar da manufarta ta bude kofa ga kasashen waje, da amfani da babbar kasuwarta ta cikin gida wajen samar da karin damammakin ci gaban tattalin arziki ga sauran kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

 

An bude bikin CIIE na bana a ranar 5 ga watan Nuwamban da muke ciki, kuma za a ci gaba da gudanar da shi, har zuwa ranar 10 ga wata, inda aka samu kamfanoni 4108 na kasashen ketare da suke baje kolin kayayyakinsu. Duk a wannan biki, kasashe 17 na nahiyar Afirka sun kafa rumfunan baje kolin kayayyakinsu, kuma adadin kamfanoni masu baje kolin kaya daga nahiyar Afirka ya karu da kashi 80% , bisa adadin na shekarar bara.

 

Me ya sa bikin CIIE ke jan hankalin kamfanonin kasashen Afirka? Domin babbar kasuwar kasar Sin, da ta kunshi mutane biliyan 1.4, ta ba da damar sayar da karin kayayyaki, tare da samun riba mai tsoka. Misali, tun bayan da busasshen tattasan Ruwanda ya shiga kasuwannin kasar Sin, bisa damar bikin CIIE na shekarar 2021, noman tattasai ya riga ya zame wa ‘yan kasar wata muhimmiyar sana’a mai alaka da fitar da kayayyaki zuwa ketare, wadda ta ba dubun dubatar manoman kasar damar wadatar da kai. Bugu da kari, a bikin CIIE na shekarar 2024, wasu kayayyakin Afirka irin su zuman Zambia, da furanni na Kenya, da abarba na kasar Benin, su ma sun fara samun karbuwa tsakanin al’ummun kasar Sin.

 

Hassan Mohammed, jami’i mai kula da aikin kasuwanci a karamin ofishin jakadancin Najeriya dake birnin Shanghai na Sin, ya ce a bikin CIIE da ya gudana a bara, kamfanoni 13 daga cikin 16 na Najeriya sun yi nasarar kulla yarjeniyoyin hadin gwiwa da abokan huldar kasar Sin, ciki har da wata kwangilar samar da tsabar koko, wadda kudinta ya kai sama da dalar Amurka miliyan 1.2. Bugu da kari, yazawa (kashu ko cashew) na Najeriya, da ba a san shi ba a baya a kasar Sin, yanzu yana kara samun karbuwa a kasar, duk albarkacin bikin CIIE.

 

Hausawa kan ce “Da abokin daka ake shan gari”. To, duk wadannan abubuwan da suka faru a bikin CIIE sun tabbatar da gaskiyar maganar. Ma iya cewa bikin ya nuna babbar ka’idar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wato samar da damammaki da amfanar da juna.

 

Sai dai, idan wani ya saba da neman sanin abubuwa game da kasar Sin ta hanyar rahotannin da kafofin watsa labaru na kasashen yamma suke bayarwa ko wallafawa, ba makawa zai cika da shakku da damuwa game da dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Saboda tunanin da Turawa ‘yan kasashen yamma suka saba da shi, ya shafi neman cin moriya da faduwar wani, da tattare samuwar dimbin albarkatu a hannun mutane kalilan, duk da cewa sauran mutane da yawa za su yi fama da talauci da yunwa.

 

Watakila wannan tunani nasu ya hana su fahimtar yanayin huldar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka na amfanin juna, da sanya su neman shafa kashin kaza ga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka. Amma kamar yadda ake cewa “Gani Ya Kori Ji”, yadda kasar Sin ke kokarin taimakon kasashen Afirka wajen neman ci gaban tattalin arziki, zai rufe bakin gulmace-gulmacen masu yada jita-jita. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Next Post
Gwamnatin tarayya

Ta'addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.