• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Bazara Na Shekarar Dabbar Loong Ya Baiwa Duniya Damar Ganin Muhimmancin Tattalin Arzikin Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bikin Bazara Na Shekarar Dabbar Loong Ya Baiwa Duniya Damar Ganin Muhimmancin Tattalin Arzikin Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a yau cewa, karuwar masu yawon bude ido na kasar Sin da na kasashen waje a lokacin bikin Bazara na shekarar dabbar Loong, ta sanya bikin Bazara ya zama kololuwar karuwar aikin yawon bude ido a duniya, da kuma baiwa duniya damar ganin ci gaban tattalin arzikin kasar Sin.

Alkaluma sun nuna cewa, a lokacin bikin Bazara, masu yawon bude ido na kasar Sin, sun kashe jimillar kudin da ya kai yuan biliyan 632.687, wanda ya karu da kashi 7.7 cikin 100 idan aka kwatanta da na shekarar 2019, yawan kudaden da aka samu a fannin gidajen sinima na kasar Sin ya zarce yuan biliyan 8, lamarin da ya karya tarihi.

  • Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Mao ta ce, kasar Sin za ta ci gaba da sa kaimi ga gudanar da mu’amalar mutane a tsakaninta da kasashen ketare, da ba da gudummawa ga kara bude kofa ga kasashen waje, da samar da yanayi mai kyau ga dukkan kasashen duniya, wajen raba damar da kasar Sin ke da ita.

Sannan game da batun ra’ayin jami’in kasar Philippines kan tsibirin Huangyan dake tekun kudancin Sin, Sin ta jaddada cewa, tsibirin Huangyan da yankunan tekun dake kewayensa mallakar kasar Sin ne.

Rahotanni na cewa, kakakin hukumar kula da kamun kifi da albarkatun ruwa ta kasar Philippines ya bayyana a ranar 17 ga wannan wata cewa, masunta na kasar Sin suna amfani da sinadarin cyanide a tsibirin Huangyan don lalata wuraren kamun kifi na kasar Philippines.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Game da wannan batu, Mao Ning ta bayyana cewa, lamarin da bangaren Philippines ya fada, ya kirkire shi ne da gangan. Gwamnatin kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan kiyaye muhallin halittu da tabbatar da albarkatun kifi, tare da dagewa wajen dakile kamun kifi ba bisa ka’ida ba.

Bugu da kari, game da Mao Ning ta gabatar da halartar ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a gun taron tsaro na Munich karo na 60, inda ta bayyana cewa, babban sakon da Wang Yi ya gabatar shi ne cewa, kasar Sin za ta ci gaba da kiyaye manyan manufofinta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko da yaushe, a cikin duniya mai fama da tashin hankali

Mao Ning ta ce, kamata ya yi hadin gwiwa da samun nasara tare, su zama tushen manufofin dukkan kasashe wajen tafiyar da harkokin kasa da kasa. Kasar Sin tana son hada kai da dukkan bangarori, don samun nasara tare, da kaucewa hasara da dama, da kara tabbatar da tabbas a duniya, da samar da makoma mai kyau ga daukacin bil-Adama. (Masu Fassarawa: IbrahimYaya, Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayyana A Ofishin Hukumar EFCC Da Ke Jihar

Next Post

Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

Related

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

15 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

16 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

17 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

18 hours ago
Bazara
Daga Birnin Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

19 hours ago
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000
Daga Birnin Sin

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

20 hours ago
Next Post
Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana 'Ƙauye Day' Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.