• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Bazara Na Shekarar Dabbar Loong Ya Baiwa Duniya Damar Ganin Muhimmancin Tattalin Arzikin Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Bikin Bazara Na Shekarar Dabbar Loong Ya Baiwa Duniya Damar Ganin Muhimmancin Tattalin Arzikin Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a yau cewa, karuwar masu yawon bude ido na kasar Sin da na kasashen waje a lokacin bikin Bazara na shekarar dabbar Loong, ta sanya bikin Bazara ya zama kololuwar karuwar aikin yawon bude ido a duniya, da kuma baiwa duniya damar ganin ci gaban tattalin arzikin kasar Sin.

Alkaluma sun nuna cewa, a lokacin bikin Bazara, masu yawon bude ido na kasar Sin, sun kashe jimillar kudin da ya kai yuan biliyan 632.687, wanda ya karu da kashi 7.7 cikin 100 idan aka kwatanta da na shekarar 2019, yawan kudaden da aka samu a fannin gidajen sinima na kasar Sin ya zarce yuan biliyan 8, lamarin da ya karya tarihi.

  • Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar
  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

Mao ta ce, kasar Sin za ta ci gaba da sa kaimi ga gudanar da mu’amalar mutane a tsakaninta da kasashen ketare, da ba da gudummawa ga kara bude kofa ga kasashen waje, da samar da yanayi mai kyau ga dukkan kasashen duniya, wajen raba damar da kasar Sin ke da ita.

Sannan game da batun ra’ayin jami’in kasar Philippines kan tsibirin Huangyan dake tekun kudancin Sin, Sin ta jaddada cewa, tsibirin Huangyan da yankunan tekun dake kewayensa mallakar kasar Sin ne.

Rahotanni na cewa, kakakin hukumar kula da kamun kifi da albarkatun ruwa ta kasar Philippines ya bayyana a ranar 17 ga wannan wata cewa, masunta na kasar Sin suna amfani da sinadarin cyanide a tsibirin Huangyan don lalata wuraren kamun kifi na kasar Philippines.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Game da wannan batu, Mao Ning ta bayyana cewa, lamarin da bangaren Philippines ya fada, ya kirkire shi ne da gangan. Gwamnatin kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan kiyaye muhallin halittu da tabbatar da albarkatun kifi, tare da dagewa wajen dakile kamun kifi ba bisa ka’ida ba.

Bugu da kari, game da Mao Ning ta gabatar da halartar ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a gun taron tsaro na Munich karo na 60, inda ta bayyana cewa, babban sakon da Wang Yi ya gabatar shi ne cewa, kasar Sin za ta ci gaba da kiyaye manyan manufofinta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko da yaushe, a cikin duniya mai fama da tashin hankali

Mao Ning ta ce, kamata ya yi hadin gwiwa da samun nasara tare, su zama tushen manufofin dukkan kasashe wajen tafiyar da harkokin kasa da kasa. Kasar Sin tana son hada kai da dukkan bangarori, don samun nasara tare, da kaucewa hasara da dama, da kara tabbatar da tabbas a duniya, da samar da makoma mai kyau ga daukacin bil-Adama. (Masu Fassarawa: IbrahimYaya, Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayyana A Ofishin Hukumar EFCC Da Ke Jihar

Next Post

Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

7 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

7 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

9 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

12 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

14 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana 'Ƙauye Day' Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.