• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin Jakadancin Kasar Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin cikar ranar kasa ta Saudiyya karo 93 a gidan Ambasadanta da ke Abuja, wanda ya samu halartar jami’an gwamnati da shugabannin ofisoshin diflomasiyya da kungiyoyin kasa da kasa da kuma ‘yan kasuwa da sauran manyan mutane.

A nasa jawabin, Jakadan Kasar Saudiyya a Nijeriya H.E. Faisal bin Ebraheem Alghamdi ya bayyana cewa, Masarautar tana bikin cika shekaru 93 na hadin kan sassan Masarautar Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud (Allah Ya jikansa) a karkashin wata kungiya mai karfi wacce aka kafa ta bisa akidar Musulunci wacce daidaito, adalci da amana suka tabbata a cikinta.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Alghamdi ya kuma bayyana cewa, akwai kyakkyawar alaka a tsakanin Masarautar da Nijeriya mai cike da tarihi wacce ta ke ta ci gaba da bunkasa tun lokacin da aka kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu a shekarar 1961. Ya kuma yi fatan alheri da nasara ga mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Yayin da yake tsokaci kan kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu, jakadan ya ce, sama da mahajjata ‘yan Nijeriya 200,000 da masu zuwa (Umara) da maziyarta sun ziyarci Masarautar a shekarar da ta gabata, kuma Masarautar ta bai wa daliban Nijeriya tallafin karatu sama da 200 don yin karatu a jami’o’in kasar daban-daban. Ya kara da cewa, yawan cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya haura Dala miliyan 600.

A kan taimakon jin kai ga al’ummar Nijeriya. Jakadan Masarautar ya bayyana cewa, Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud (Allah Ya kare shi) ya ba da umarnin aiwatar da taimakon sa-kai na Nur-Saudi a Nijeriya, wanda aka fara aiwatarwa mataki-mataki; An aiwatar da matakin farko wanda aka nufi yakar makanta da musabbabanta, sannan kuma ta yi wasu ayyukan tiyata musamman a bangaren mafitsara da raba tagwayen da aka haifa a Jone.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Jakadan ya taya iyayen tagwayen murna da aka yi nasarar raba su a watan Mayun da ya gabata, a aikin tiyata mai lamba 56 da masarautar ta yi wajen raba wasu tagwaye daga sassan duniya.

A karshe, jakadan ya mika godiya ga kasashen duniya da abokan arziki daga ciki har da tarayyar Nijeriya bisa goyon bayan da ta bai wa Saudiyya na karbar bakuncin bikin baje kolin duniya na 2030 a birnin Riyadh, wanda ya zo daidai da ranar da Saudiyya ta ke shirin kaddamar da kudirinta na shekarar 2030.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

Next Post

Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Saudiyya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post
Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.