• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Ya Kamata A Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin Jakadancin Kasar Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin cikar ranar kasa ta Saudiyya karo 93 a gidan Ambasadanta da ke Abuja, wanda ya samu halartar jami’an gwamnati da shugabannin ofisoshin diflomasiyya da kungiyoyin kasa da kasa da kuma ‘yan kasuwa da sauran manyan mutane.

A nasa jawabin, Jakadan Kasar Saudiyya a Nijeriya H.E. Faisal bin Ebraheem Alghamdi ya bayyana cewa, Masarautar tana bikin cika shekaru 93 na hadin kan sassan Masarautar Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud (Allah Ya jikansa) a karkashin wata kungiya mai karfi wacce aka kafa ta bisa akidar Musulunci wacce daidaito, adalci da amana suka tabbata a cikinta.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Alghamdi ya kuma bayyana cewa, akwai kyakkyawar alaka a tsakanin Masarautar da Nijeriya mai cike da tarihi wacce ta ke ta ci gaba da bunkasa tun lokacin da aka kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu a shekarar 1961. Ya kuma yi fatan alheri da nasara ga mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Yayin da yake tsokaci kan kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu, jakadan ya ce, sama da mahajjata ‘yan Nijeriya 200,000 da masu zuwa (Umara) da maziyarta sun ziyarci Masarautar a shekarar da ta gabata, kuma Masarautar ta bai wa daliban Nijeriya tallafin karatu sama da 200 don yin karatu a jami’o’in kasar daban-daban. Ya kara da cewa, yawan cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya haura Dala miliyan 600.

A kan taimakon jin kai ga al’ummar Nijeriya. Jakadan Masarautar ya bayyana cewa, Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud (Allah Ya kare shi) ya ba da umarnin aiwatar da taimakon sa-kai na Nur-Saudi a Nijeriya, wanda aka fara aiwatarwa mataki-mataki; An aiwatar da matakin farko wanda aka nufi yakar makanta da musabbabanta, sannan kuma ta yi wasu ayyukan tiyata musamman a bangaren mafitsara da raba tagwayen da aka haifa a Jone.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Jakadan ya taya iyayen tagwayen murna da aka yi nasarar raba su a watan Mayun da ya gabata, a aikin tiyata mai lamba 56 da masarautar ta yi wajen raba wasu tagwaye daga sassan duniya.

A karshe, jakadan ya mika godiya ga kasashen duniya da abokan arziki daga ciki har da tarayyar Nijeriya bisa goyon bayan da ta bai wa Saudiyya na karbar bakuncin bikin baje kolin duniya na 2030 a birnin Riyadh, wanda ya zo daidai da ranar da Saudiyya ta ke shirin kaddamar da kudirinta na shekarar 2030.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cibiyar Binciken Harkar Noma (IAR) Ta Samar Da Irin Masara Mai Inganci

Next Post

Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

Related

Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

1 hour ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

4 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

6 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

7 hours ago
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

8 hours ago
Next Post
Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya Za Ta Sayo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu 12

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

August 12, 2025
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.