• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sauyin yanayi

Matsalar sauyin yanayi ta ci gaba da shafar duk fadin duniya a halin yanzu, inda ake kara bukatar karfin gwiwa da daukar matakai na zahiri don tinkarar matsalar. Kafar watsa labarai ta CGTN dake karkashin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, ya hada kai tare da jami’ar Renmin ta kasar Sin, don gudanar da wani binciken jin ra’ayin al’umma dake kunshe da mutane 7658 daga kasashe 38, inda kaso 90.3 bisa dari na masu ba da amsa a binciken ke ganin cewa, akwai bukatar shawo kan matsalar sauyin yanayi ba tare da bata lokaci ba, kana ya zama dole sassan kasa da kasa su cimma matsaya tare da kara daukar matakai na zahiri.

 

Yarjejeniyar tinkarar matsalar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, a tarihi da kuma a halin yanzu, kasashen da suka fi fitar da hayaki mai gurbata muhalli, kasashe ne masu hannu da shuni, don haka an tsara wata manufa dake cewa, kasashe masu arziki da kasashe masu tasowa, ya kamata su dauki nauyin shawo kan matsalar sauyin yanayi tare, amma akwai bambancin nauyin dake wuyan kowa. Sakamakon binciken ya kuma nuna cewa, kaso 75.3 bisa dari na masu ba da amsa na ganin cewa, kasashe masu arziki ba su nuna sahihiyar aniya ko daukar matakai na zahiri a fannin tinkarar sauyin yanayi dake addabar duniya ba, al’amarin da ya raunata hadin-gwiwar kasa da kasa wajen shawo kan matsalar sauyin yanayi. Sai kuma kaso 73.9 bisa dari dake ganin cewa, kasa cika alkawarin tallafa wa ayyukan tinkarar matsalar sauyin yanayi da kasashe masu hannu da shuni suka yi, abu ne dake nuna kin sauke nauyin da ya rataya da su. Sa’annan kaso 85.8 bisa dari na masu ba da amsar sun bukaci kasashe masu arziki, da su samar da tallafin kudi mai tsoka ga kasashe masu tasowa, don aiwatar da yarjejeniyar Paris a zahirance.

 

Daga cikin masu ba da amsa a binciken, akwai wadanda suka fito daga kasashe masu arziki, ciki har da Amurka, da Jamus, da Japan, akwai kuma wadanda suka fito daga kasashe masu tasowa, ciki har da Argentina, da Indiya, da kuma Kenya. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.