• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar sauyin yanayi ta ci gaba da shafar duk fadin duniya a halin yanzu, inda ake kara bukatar karfin gwiwa da daukar matakai na zahiri don tinkarar matsalar. Kafar watsa labarai ta CGTN dake karkashin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, ya hada kai tare da jami’ar Renmin ta kasar Sin, don gudanar da wani binciken jin ra’ayin al’umma dake kunshe da mutane 7658 daga kasashe 38, inda kaso 90.3 bisa dari na masu ba da amsa a binciken ke ganin cewa, akwai bukatar shawo kan matsalar sauyin yanayi ba tare da bata lokaci ba, kana ya zama dole sassan kasa da kasa su cimma matsaya tare da kara daukar matakai na zahiri.

 

Yarjejeniyar tinkarar matsalar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, a tarihi da kuma a halin yanzu, kasashen da suka fi fitar da hayaki mai gurbata muhalli, kasashe ne masu hannu da shuni, don haka an tsara wata manufa dake cewa, kasashe masu arziki da kasashe masu tasowa, ya kamata su dauki nauyin shawo kan matsalar sauyin yanayi tare, amma akwai bambancin nauyin dake wuyan kowa. Sakamakon binciken ya kuma nuna cewa, kaso 75.3 bisa dari na masu ba da amsa na ganin cewa, kasashe masu arziki ba su nuna sahihiyar aniya ko daukar matakai na zahiri a fannin tinkarar sauyin yanayi dake addabar duniya ba, al’amarin da ya raunata hadin-gwiwar kasa da kasa wajen shawo kan matsalar sauyin yanayi. Sai kuma kaso 73.9 bisa dari dake ganin cewa, kasa cika alkawarin tallafa wa ayyukan tinkarar matsalar sauyin yanayi da kasashe masu hannu da shuni suka yi, abu ne dake nuna kin sauke nauyin da ya rataya da su. Sa’annan kaso 85.8 bisa dari na masu ba da amsar sun bukaci kasashe masu arziki, da su samar da tallafin kudi mai tsoka ga kasashe masu tasowa, don aiwatar da yarjejeniyar Paris a zahirance.

 

Daga cikin masu ba da amsa a binciken, akwai wadanda suka fito daga kasashe masu arziki, ciki har da Amurka, da Jamus, da Japan, akwai kuma wadanda suka fito daga kasashe masu tasowa, ciki har da Argentina, da Indiya, da kuma Kenya. (Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya

Next Post

Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

18 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

19 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

19 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

20 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

22 hours ago
Next Post
Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.