• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar sauyin yanayi ta ci gaba da shafar duk fadin duniya a halin yanzu, inda ake kara bukatar karfin gwiwa da daukar matakai na zahiri don tinkarar matsalar. Kafar watsa labarai ta CGTN dake karkashin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, ya hada kai tare da jami’ar Renmin ta kasar Sin, don gudanar da wani binciken jin ra’ayin al’umma dake kunshe da mutane 7658 daga kasashe 38, inda kaso 90.3 bisa dari na masu ba da amsa a binciken ke ganin cewa, akwai bukatar shawo kan matsalar sauyin yanayi ba tare da bata lokaci ba, kana ya zama dole sassan kasa da kasa su cimma matsaya tare da kara daukar matakai na zahiri.

 

Yarjejeniyar tinkarar matsalar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, a tarihi da kuma a halin yanzu, kasashen da suka fi fitar da hayaki mai gurbata muhalli, kasashe ne masu hannu da shuni, don haka an tsara wata manufa dake cewa, kasashe masu arziki da kasashe masu tasowa, ya kamata su dauki nauyin shawo kan matsalar sauyin yanayi tare, amma akwai bambancin nauyin dake wuyan kowa. Sakamakon binciken ya kuma nuna cewa, kaso 75.3 bisa dari na masu ba da amsa na ganin cewa, kasashe masu arziki ba su nuna sahihiyar aniya ko daukar matakai na zahiri a fannin tinkarar sauyin yanayi dake addabar duniya ba, al’amarin da ya raunata hadin-gwiwar kasa da kasa wajen shawo kan matsalar sauyin yanayi. Sai kuma kaso 73.9 bisa dari dake ganin cewa, kasa cika alkawarin tallafa wa ayyukan tinkarar matsalar sauyin yanayi da kasashe masu hannu da shuni suka yi, abu ne dake nuna kin sauke nauyin da ya rataya da su. Sa’annan kaso 85.8 bisa dari na masu ba da amsar sun bukaci kasashe masu arziki, da su samar da tallafin kudi mai tsoka ga kasashe masu tasowa, don aiwatar da yarjejeniyar Paris a zahirance.

 

Daga cikin masu ba da amsa a binciken, akwai wadanda suka fito daga kasashe masu arziki, ciki har da Amurka, da Jamus, da Japan, akwai kuma wadanda suka fito daga kasashe masu tasowa, ciki har da Argentina, da Indiya, da kuma Kenya. (Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya

Next Post

Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

21 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

22 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

23 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

24 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

1 day ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

Xi: Kasar Sin Ta Shirya Tsaf Don Samun Nasarar Hadin Gwiwar Kasashe Tare Da Peru

LABARAI MASU NASABA

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.