• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

by Bello Hamza and Sulaiman
2 hours ago
Dantsoho

Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana cewa, bisa yadda aka tsara yanayin Birnin Tarayyar Abuja da kuma yadda birnin ya kasance, yana da albarkatun noma, hakan zai bai wa Hukumar NPA damar ci gaba da wata karfafa kokarin Gwamnatin Tarayya na, bunkasa samar da kudaden shiga, daga fannin da bai bai shafi harkar Man Fetur ba.

 

Dantsoho a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis a da ta gabata, taron baje koli na kasa da kasa da cibiyar kasuwanci ta Abuja ta shirya ya ce, kasancewar birnin a tsakiyar kasar nan, hakan zai kuma taimaka wa Hukumarsa, cimma kudurinta na kara habaka hada-hadar kasuwanci.

  • An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
  • Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

“Kasancewar yanayin na Abuja za ta samar da damar amfana a bangaren hada-hadar fitar da kaya daga cikin kasar nan, zuwa ketare”Inji Dantsoho.

 

LABARAI MASU NASABA

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Shugaban ya ci gaba da cewa, a karkashin shugabancinsa, Hukumar za ta yi namijin kokari wajen bayar da goyon bayanta, wajen fitar da kayan da ba su shafi dangogin Mai ba, zuwa kasar waje, musamman ta hanyar cin giyar albakatun yanayin na Abuja da kuma na bangaren aikin noma, da birnin ke da shi. Ya kara da cewa, ta hanyar wadannan alkatun kasar da birnin ke da su, Hukumar za ta kara bayar da gudunmwarta, wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar nan da kuma kara fitar da kayan da ba su shafi Man ba, zuwa ketare.

 

A cewarsa, domin Hukumar ta tabbatar da na kara mayar da hankalin wajen ganin ana bin ka’ida da kuma tabbatar da ingancin gudanar da ayyukanta, ta kirkiro da tsare-tsare na fasahar zamani na bai daya da ake kira a turance, PCS da kuma NSW.

A cewarsa, wadannan fasahar ta zamani, za su taimaka wajen hada masu ruwa da tsaki a fannin da ke fitar da kaya zuwa ketare tare da kuma rage jinkiri wajen fitar da kayan waje da kuma samar da kyakyawan yanayi ga masu fitar da kayan ketare.Shugaban ya sanar da cewa, Hukumar na alfaharin danganta manta da ayyukan da Cibiyar ta kolin kasuwanci ta Abuja ke ci gaba da gudanarwa musamman a bangaren kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

Dantsoho ya kuma gayyaci masu ruwa da tsaki a fannin kar su bari a barsu a baya, wajen cin gajiyar saukin da Hukumar ta samar na fitar da kaya daga cikin kasar nan, zuwa ketare.

Kazalika, Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar ta kuma samar da tsarin fasahar zamani na fitar da kaya a cikin sauki a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar wato EPT.

Ya kara da cewa, wannan fasahar ta taimaka matuka wajen fitar da kaya waje ba tare da wani tarnaki ba.

Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta kuma fadada fasahar ta EPT, domin samar da saukin fitar da kaya ga kananan da matsakaitan masana’antun kasar suka sarrafa, domin fitar da su ketare.

Hakazalika, Shugaban ya bayyana cewa, domin ayyukan Hukumar su tafi kafada da kafada da kudurin Gwamnatin Tarayya NPA ta saita gudanar da ayyukanta ta hanyar yin amfani da fasahar ta zamani ta PCS.

A cewarsa, wannan zai tabbatar da samar da wani ginshike ga fasahar NSW, inda za a rinka fitar da kayan waje, ba tare da wata matsala ba.

Dantsoho ya yi nuni da cewa, fasahar ta NSW aba ce, da ake yin amfani da da ita, a daukacin fadin duniya, wajen samar da saukin fitar da kaya waje.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Hukumar na daukar Malamai wajen ganin cewa, ayyukanta, sun kai da lungu da sako, da ke da wuyar isa a kasar.

Ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yau, kofar Hukumar a bude take domin yin hadaka da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
Tattalin Arziki

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi
Tattalin Arziki

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Next Post
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.