• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 2

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gaggauta Buɗa-baki yana tabbatar da mutane a kan sunna. Akwai hadisai a kan haka:

1.  An karɓo hadisi daga Sahlu dan Sa’adu Allah Ya ƙara yarda a gare shi, ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Al’ummata ba za ta gushe a kan sunnata ba, matuƙar ba ta jirkinta buɗa-bakinta zuwa fitowar taurari ba “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan yana azumi sai ya umarci wani mutum ya hau wani abu mai tudu ya ga rana ta faɗi, idan ta fadi sai ya yi buɗa-baki.  Hadisi ne ingantacce Ibnu Khumaima ne yabruwaito [#2061] da Ibnu Hibbãn [#3510] da Hãkim [#1584].

  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

2. An karɓo hadisi daga Anas dan Malik Allah Ya ƙara yarda a gare shi ya ce: “Ban taɓa ganin Manzon Allah Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam ya yi sallar magriba ba (alhali yana azumi)  face sai ya yi buɗa-baki ko da kuwa da maƙwalwar ruwa ne “Hadisi ne ingantacce Ibnu Hibbãn [#3504] da Abu Ya’alã [#3792] da Ibnu Khuzaima [#2063] da Bazzãr [#7127].

Jinkirta ta buɗa-baki saɓa wa sunnar Manzon Allah sallallahu alaihi wa alihi wa sallam ne, kuma mutane ba za su gushe ba cikin alheri matuƙar suka aikata sunna. Duba Ibnu Dakikil Id; Ihkãmul Ahkãm [shafi na 419].

Kuma jirkinta buɗa-baki koyi ne da ahlulkitãbi, watau Yahudu da Nasara kamar yadda ya gabata a hadisi. A cikin Musulumi an samu waɗanda suke kwaikwayon Yahudu da Nasara wajen jinkirta buɗa-baki, ba sa gaggauta yinsa, waɗannan mutane su ne ‘yan Shi’a, kuma suna ƙudurce jinkirta shi, shi ne daidai. Waɗannan hadisai da aka ambata suna yi musu martani.

Labarai Masu Nasaba

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jinkirta buɗa-baki alama ce ta ‘yan bidi’a. Duba as-San’ani; Subus Salam [2/221].

Imam as-Shãfi’i Allah ya yi masa rahama yana cewa: “Ina son gaggauta buɗa-baki, da ƙin jirkinta shi, kuma ina ƙyamar hakan ne ga wanda ya jinkirta shi da gangan kuma yake ganin haka shi ne abin da ya fi falala” Duba as-Shãfi’i; al-Ummu [2/106].


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AzumiBUƊA-BAKIRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Next Post

Ramadan: Sanata Yari Ya Buƙaci Musulmi Da Su Yi Wa Shugaba Tinubu Addu’a

Related

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

12 hours ago
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

2 days ago
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano
Bakon Marubuci

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

3 days ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Me Ake Nufi Da Ado? 
Bakon Marubuci

Me Ake Nufi Da Ado? 

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Next Post
Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Ramadan: Sanata Yari Ya Buƙaci Musulmi Da Su Yi Wa Shugaba Tinubu Addu'a

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.