• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

by Abba Ibrahim Wada and Muhammad
2 days ago
in Labarai
0
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, ya bayyana marigayi tsohon shugaban ƙasa,  Muhammad Buhari a matsayin ɗan kishin ƙasa, soja kuma dattijo, wanda ya hidimtawa ƙasa cikin girma da daraja da kuma gaskiya da riƙon amana da sadaukarwa.

A wata sanarwa da shugaban ƙasar ya sanyawa hannu da kansa, Tunubu ya sanar da rasuwar tsohon shugaban a wani asibiti a birnin Landan a yau Lahadi 12, Yuli 2025.

  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan
  • Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

“Na kaɗu sosai da samun labarin rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammad Buhari, wanda na gada, wanda ya koma ga mahaliccinsa a yau” cewar shugaba Tinubu

Shugaban ya bayyana rayuwar Buhari a matsayin babban rashin wanda ya yi wa ƙasa hidima, daraja da kuma sadaukar da kai wajen haɗin kan ƙasa da ci gabanta.

Shugaba Tinubu ya ce Buhari ya mulki Nijeriya a lokaci mai tsauri, na farko a lokacin mulkin soja da kuma farar hula, kuma ya yi mulkin bisa adalci da ƙwarin guiwa da kuma gaskiya tare da yaƙinin cewa Nijeriya za ta samu ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

Tinubu ya ce sun yi magana da matar marigayin, Hajiya Aisha Buhari kuma ya yi mata ta’aziyya,  sannan ya yi wa gaba ɗaya danginsa ta’aziyyar rasuwar Buhari da ƴan Nijeriya baki ɗaya.

Shugaban ƙasar ya kuma miƙa saƙon ta’aziyya ga gwamnatin jihar Katsina da al’ummar jihar, musamman masarautar Daura, inda Buhari ya taso.

Tuni dai shugaban ya bayar da umarnin sakko da tutar Nijeriya ƙasa-ƙasa na tsawon kwanaki bakwai daga yau, duka a cikin jimamin rasuwar Buharin.

Shugaban ƙasa,  Bola Tinubu ya kuma bayar da sanarwar taron gaggawa na majalisar zartarwa ta ƙasa ranar Talata domin domin girmama marigayi Buhari.

Tinubu ya bayar da sanarwar cewa gwamnatin tarayya za ta karrama Buhari da lambar yabo domin girmama irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban ƙasa.

Marigayi Muhammad Buhari dai ya rasu yana da shekara 82 a duniya, bayan ya sha jinya a birnin Landan na ƙasar Ingila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariLandanNijeriyaRasuwaRasuwar BuhariTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

Next Post

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Related

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

55 minutes ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

3 hours ago
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Manyan Labarai

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

4 hours ago
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

12 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

13 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

16 hours ago
Next Post
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

July 16, 2025
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

July 16, 2025
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.