• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

by Abba Ibrahim Wada and Muhammad
7 hours ago
in Labarai
0
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, ya bayyana marigayi tsohon shugaban ƙasa,  Muhammad Buhari a matsayin ɗan kishin ƙasa, soja kuma dattijo, wanda ya hidimtawa ƙasa cikin girma da daraja da kuma gaskiya da riƙon amana da sadaukarwa.

A wata sanarwa da shugaban ƙasar ya sanyawa hannu da kansa, Tunubu ya sanar da rasuwar tsohon shugaban a wani asibiti a birnin Landan a yau Lahadi 12, Yuli 2025.

  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan
  • Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

“Na kaɗu sosai da samun labarin rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammad Buhari, wanda na gada, wanda ya koma ga mahaliccinsa a yau” cewar shugaba Tinubu

Shugaban ya bayyana rayuwar Buhari a matsayin babban rashin wanda ya yi wa ƙasa hidima, daraja da kuma sadaukar da kai wajen haɗin kan ƙasa da ci gabanta.

Shugaba Tinubu ya ce Buhari ya mulki Nijeriya a lokaci mai tsauri, na farko a lokacin mulkin soja da kuma farar hula, kuma ya yi mulkin bisa adalci da ƙwarin guiwa da kuma gaskiya tare da yaƙinin cewa Nijeriya za ta samu ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Tinubu ya ce sun yi magana da matar marigayin, Hajiya Aisha Buhari kuma ya yi mata ta’aziyya,  sannan ya yi wa gaba ɗaya danginsa ta’aziyyar rasuwar Buhari da ƴan Nijeriya baki ɗaya.

Shugaban ƙasar ya kuma miƙa saƙon ta’aziyya ga gwamnatin jihar Katsina da al’ummar jihar, musamman masarautar Daura, inda Buhari ya taso.

Tuni dai shugaban ya bayar da umarnin sakko da tutar Nijeriya ƙasa-ƙasa na tsawon kwanaki bakwai daga yau, duka a cikin jimamin rasuwar Buharin.

Shugaban ƙasa,  Bola Tinubu ya kuma bayar da sanarwar taron gaggawa na majalisar zartarwa ta ƙasa ranar Talata domin domin girmama marigayi Buhari.

Tinubu ya bayar da sanarwar cewa gwamnatin tarayya za ta karrama Buhari da lambar yabo domin girmama irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban ƙasa.

Marigayi Muhammad Buhari dai ya rasu yana da shekara 82 a duniya, bayan ya sha jinya a birnin Landan na ƙasar Ingila.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariLandanNijeriyaRasuwaRasuwar BuhariTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

Next Post

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Related

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan
Labarai

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

6 hours ago
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo
Labarai

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

6 hours ago
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan
Labarai

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

7 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Labarai

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

7 hours ago
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan
Labarai

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

8 hours ago
Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa
Labarai

Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

8 hours ago
Next Post
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

July 13, 2025
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

July 13, 2025
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

July 13, 2025
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

July 13, 2025
Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

July 13, 2025
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

July 13, 2025
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

July 13, 2025
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

July 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.