• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Bai Wa Mata Kulawar Da Ta Dace Lokacin Juna Biyu Da Haihuwa

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Taskira
0
Bukatar Bai Wa Mata Kulawar Da Ta Dace Lokacin Juna Biyu Da Haihuwa

Princess Fatima Zahra

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

Barkanku da kasancewa tare da shafin Taskira, shafin da ke zakulo muku batutuwa daban-daban da suka shafi al’umma. Tsokacin mu na yau zai yi duba ne game da wasu matsaloli wanda Mata ke fuskanta a wajen mazajensu yayin da suke dauke da juna biyu ko kuma bayan haihuwa. Idan aka yi duba da matan da ke zuwa asibiti domin rainon ciki (Awo) ko haihuwa, za a ga mafi yawan mata na fuskantar kalubale na rashin kulawar da ya kamata mazajensu su ba su a yayin da suke dauke da juna biyu ko lokacin da suke yunkurin saukewa. Mafi yawan maza na kin bawa matansu kulawar da ta dace musamman wajen siyen magunguna ko ba da kudin hoton ciki, da dai sauran abubuwan da suka kamata a yi wa matar a asibiti. Akwai abubuwa da dama wanda wasu mazan ke bi dan cutar da matansu yayin da suke dauke da ciki tamkar cikin ba nasu ba ne, wani asibitin ma ba zai bar matar ta je ba in kuwa ta je to a boye ne. Wani kuma zai bar ta ta je amma fucikarsa ba za ta yi magani ba, kuma yana da shi ba wai babu ba, wani namijin kuma a kullum ba shi da aiki sai duka ko zagi, tsana ta shiga tsakani sabida tana dauke da ciki, kamar wadda ta fita tayyo.

Wani idan matarsa za ta haihu a lokacin za a neme shi a rasa ko a waya ba za a iya samunsa ba, sabida biyan kudi da sauran abubuwan da za a iya bukata alhalin yana da kudin, wani ma sai dai ta ji labarin cewa daga asibitin ta wuce gidansu ya saketa, ba don komai ba sai dan yana jin nauyi ya karu akansa, wanda inda za a buncika wani ko ta nemi tayi tazarar haihuwa ba zai taba bari ba, amma kuma duk haihuwa da rainon ciki haka take fama a wajensa. Dalilin hakan ya sa shafin Taskira jin ta bakin wasu daga cikin mabiyansa game da wannan matsala, Ko laifin waye tsakanin Mijin da Matar? Me yake janyo hakan kuma ta wacce hanya za a magance matsalar? Ga dai ra’ayoyin nasu kamar haka:

Sunana Princess Fatimah Zahra Mazadu Gomben Lanjeriya:

Juna Biyu
Princess Fatima Zahra

Gaskiya abun da zan ce ya buwayi duniya dan mazajen yanzu rayuwa suke da auren sha’awa yawanci. Mafi akasarin maza basa murna da yawan haihuwa wannan haka ne ‘more especially’ in an haifi ba abun da suke so ba, misali namiji yake so kika haifi mace. Ciki wasu mata suna kurewa maza maleji ne da munafunci da son tara abun duniya ta hanyar langwabewa yau jinya gobe ciwo, wasu kuma kazantar banza da rashin kulawa da miji. Dukkansu dan kai kayi cikin bai kamata ka nuna kyama ba, ita ai mace in ka ga ba ta son haihuwa toh rashin rabon gaggawa ne, ko shi mijin dan son rayuwa ne dole ta dakata in bata son komawa gidansu. Hanya daya ce in baka son haihuwa kar ka yi aure, dan ba wanda bai sha’awar ajiye zuriya, kai da ba a haihuwa za a haife ka? Dan a zahiri wallahi mata basu cika kin haihuwa ba, sai dai maza su yaudare su su bata musu rayuwa na har abada da kwayoyin hana haihuwa. Allah ya shirya su, amma kira na ga mata da ki rasa mahaifarki ko ki lalata rayuwar ki gwara ki ji kunyar mutanen duniya ki dawo zawarci Allah zai baki mai son tara zuriya, in fannin namiji ne ya kiyaye dan ba dawwama za ka yi a duniya ba, kana son mai maka addu’a da wanda za ka barwa duk wata amana ta rayuwa, ciki wahala ne dan Allah maza ana tausayin mata, wallahi ka ga mace na tafiya wata sai ka zubar mata da hawaye, wata kuma in tana bed rest sai ka tausayamata. Ku ji tsoron Allah ku ji tausayin matanku ko dan gobe kiyama su yi alfahari da ku, mata a daure dan kin yi ciki ba zai hana ki yi wa mijinki biyayya ba ko dan lahirarki tayi kyeu. Muhayyafa mu cika umurni da fadin Manzon Allah (S. A. W).

Sunana Mas’ud Saleh Dokatawa:

Juna Biyu
Mas’ud Saleh Dokadawa

Wannan halayen banza abu ne mara kyau, sannan rashin sanin hakkin aure ne, kuma ya sabawa al’adar malam bahaushe, idan mutum bai yi wa matarsa abin da ya zama wajibi ba na kula da lafiya daga daukan ciki har zuwa haihuwa ba, lallai zai gamu da fushin Allah. Sannan ba zai ga da kyau ba shi ma saboda rashin sauke nauyin da Allah ya dora masa matukar yanada halin yin hakan, sannan ko ba da kudi ba akwai kulawa ta daban wacce zai iya yi. Laifin na maza ne, indai ba cikin shege bane ai bai kamata maza su yi wa matan haka ba. Abin da ke jawo hakan shi ne; Wasu matan sukan zama kazamai idan cikinsu yayi girma basa iya tsabtace jikinsu da muhallinsu. Sannan wasu mazan sukan yi hakanne saboda ba a son ransu matan suka dauki cikin ba don haka suke yi musu wulakanci, wasu mazan kuma suna zargin matan akan cikin ya sa suke gudarsu har bayan haihuwa. Hanyar magancewa shi ne; Maza su ji tsoron Allah su sani cewa za a tambayesu akan duk abin da aka basu kiwo, su kuma matan su rinka kulawa da kansu akan tsafta da kula da jikinsu da kuma kaucewa dukkan abin da zai iya kawo zargi a tsakanin zamansu. Shawara ita ce su ji tsoron Allah su daina, sannan kuma su kiyaye hakkokin iyalensu kada suyi abin da zai batawa matansu rai da gangan, sannan mata suna da bukatar kulawa a koda yaushe.

Sunana Musbahu Muhammad Gorondutse:

Juna Biyu
Musbahu Muhammad

Rashin tausayi da cikakken ilimin addini dana zamani shi yake haifar da haka. Laifin miji ya fi yawa, amma sai dai suma matan ya kamata su duba a inda suka gaza su gyara kuma su dinga yawaita addu’a. Namiji ya kamata ya san cewa ita matar amanar Allah ce a hannunsa dan haka duk abin da yayi mata sai Allah yayi musu hisabi, kuma ya tuna shi ma zai iya haifar ‘ya Mace ba zai so a yi wa ‘yarsa hakan ba. Shawara su ji tsoron Allah su daina hakan, sabida farin cikin matar shi ne farin cikinsa. Sannan su kansu ‘ya’yansu sai sun fi kaunarsa idan suna zaman lafiya da matarsa.

Sunana Abba Abubakar Yakubu, Marubuci, Dan Jarida, daga Jos ta Arewa, a Jihar Filato:

Juna Biyu
Abba Abubakar Yakubu

Na so in yi sharhi kan wannan muhimmin darasin, saboda abu ne da ya dade yana ci min tuwo a kwarya. Wasu maza masu aure suna yin wasu abubuwa da za a iya fassara shi da rashin kulawa, rashin nuna kauna, da rashin nuna dattako ga matansu, musamman a lokacin da suke cikin lalurar rashin lafiya, ko yayin haihuwa. Duk wani magidanci ya san irin dawainiya da kokari da mata ke yi a cikin gidaje da dakinansu na aure, wajen kula da iyalansu, tarbiyyar yara da hidimar kula da bukatun maigida. Don haka a duk lokacin da Allah ya jarabce su da wata lalura ta rashin lafiya, mu nuna musu tausayawa, tattali, da taimaka musu, wajen taya su wasu ayyuka ko dauke musu wasu É—awainiyoyin har su samu lafiya. A duk lokacin da suke dauke da juna biyu mu tabbatar da mun ba su kulawa ta musamman, daga abin da za su ci, yadda za su kula da kansu, da kuma uwa-uba zuwa asibiti domin yin awu da duba lafiyarta da jaririn da za ta haifa. Kuskure ne babba a ce ba ma nuna damuwa ga wannan muhimmin bangare, alhalin mu ne muka sa su cikin laulayi da dawainiyoyin da suke fama da su na rainon ciki. Haka kuma yana da muhimmanci sosai, idan lokacin haihuwarta ya yi maigida ya kasance kusa da ita, don ba ta kwarin gwiwa da nuna mata kulawa, har ta samu kanta lafiya. Kuma mu yi iya kokarin mu wajen ba ta kulawar da ta kamata, na lafiya da abin da za ta ci ta samu kwarin gwiwar shayar da abin da ta haifa. Ba koyaushe ba ne kudi ke ya ye damuwa, amma nuna kauna da kulawa, da bai wa mutum muhimmanci yana sa ya ji a ransa lallai yana da bangon jingina, kuma ana son shi. Wannan kuma ya hada har da su matan, domin akasarin korafin da maza ke yi shi ne, mata ba sa yabawa da kokarin da suke yi, duk fafutuka da sadaukarwar da suke yi a kan hidimar iyalinsa, matansu na rainawa. Ba sa yaba musu, har ma da cewa ai hakkinsu ne, ba sa bukatar a yi musu godiya. Gaskiya wannan kuskure ne, don ko Allah Ubangiji ya ce da bayinsa idan kun gode min zan kara muku!. Ya kamata mu rika yabawa da kokarin juna da nuna kauna da tausayawa a kowanne hali.

Sunana Deejat Thani daga Jihar Niger, Minna:

Juna Biyu
Deejat Thani

Idan za a fadi gaskiya in akwai so da kauna, tausayi da kuma ilimi, ai mace mai ciki abin tausayi ce a gun kowa bare mijinta. Tare kuka yi babyn nan toh ko ma menene ya kamata ace zuciyarka tana ciki da tausayin ta, in babu soyayya akwai tausayi. In kuma da ilimi duk saura mutum ba zai rasa su ba, dan ko tunani hakkinta da ke kanka ya isheka ka saukaka mata wahalar. Gaskiya laifinsu ne su biyu, abin da za a kira hakan wasu za su ce yahudanci amma a gani na wannan dabara ce. Kafin kuyi aure akwai abubuwa da dama da ya kamata ta yi yarjejeniya akai ku kuma kuyi magana akai cikinsu kuwa har da lokacin daukan ciki, guda nawa kuke su da yadda za ku dauki nauyinsu, ‘like’ in kun kawo irin wannan maganar rayuwan ki will be in balance, sai kuyi abinku tare. Musamman ma da cewa akwai hanyoyin taimakawa ga faruwan hakan. Gaskiya rashin ‘communication’ magana tsakanin ma’aurantan ke janyo matsalar nan. Komai kankantar

magana ku zauna kuyi shi gudun kar ya girma ya zama babba kin san me yake so, yadda yake so, yadda za ku ciyo kan matsalar dan kar aji bakinku. Shawara na gare ku masu dabi’un nan shi ne; kusa wa zuciyar ku hakuri babu abin da ya fi karfin Allah, idan kuma kagan abu ya same ku, ka kaddara haka yake rubuce a littafinka. Mu nemi ilimin abubuwa kafin mu yi su, kar mu biye wa wannan haka yayi, ni ma haka zan yi.

Sunana Ibraheem Ismail Ibraheem daga Jihar Kano:

Juna Biyu
Ibrahim Isma’il Ibrahim

Rashin sanin darajar mace ce da kuma rashin adalci, yin hakan yana jawo rashin zaman lafiya, da rashin mutunta juna, Laifin na maza ne masu irin wannan halayyar, yadda za a magance shi ne; Gyrawa ta hanyar kyautatawa, Allah ya sa za mu ji mu gyara.

Sunana Abdulrrashid Haruna daga Jihar Kano Nassarawa LGA:

Juna Biyu
Abdulrashid Haruna

Gaskiya wannan ba komai bane face sakaci da rashin kula, wanda hakan ba karamin cutarwa bane a zamantakewar miji da mata, sannan hakan ya sabawa amanar ta da aka baka kuma Allah ba zai bar duk mai wannan hali ba, dan farali ne ga miji kula da matarsa. Laifin Miji ne,abin da ke janyo hakan ayi Auren ba tare da yana santa ba, Ma’ana ya zama dama can ita ce take san shi, ko ya zama Auren dole aka yi musu. Gaskiya shawara gare su su ji tsoran Allah su tuna Allah bai ce ayi Aure ba muddin ba za a yi adalci ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HaihuwaJuna BiyuKulawaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Gano Shirin Da Wasu Ke Yi Na Bata Sunan Gwamnatin Tinubu Kan Cafke Emefiele

Next Post

Yadda Aikin Tituna Ya Janyo Tono Gawarwarki A Alkahira Ta Masar

Related

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
Taskira

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

5 days ago
Taskira

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

2 weeks ago
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
Taskira

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

2 weeks ago
Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
Taskira

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

1 month ago
Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
Taskira

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

2 months ago
Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
Taskira

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

2 months ago
Next Post
Yadda Aikin Tituna Ya Janyo Tono Gawarwarki A Alkahira Ta Masar

Yadda Aikin Tituna Ya Janyo Tono Gawarwarki A Alkahira Ta Masar

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.