ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
11 months ago
tallafi

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da cewa, zai kakabawa Bakununan Kasuwanci na kasar tarar Naira miliyan 150, idan aka same su suna taimakawa wajen sayar da sabbin takardun kudade.

Kazalika, Bankin na CBN, ya kuma sanar da cewa, zai hukunta ‘yan koren wadannan bankunan da ke sayar da sabbin takardun kudin.

  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC
  • Wolves Ta Naɗa Vitor Pereira A Matsayin Sabon Kocinta

Mukaddashin riko na sashen gudanar da ayyuka na Bankin Solaja Mohammed J. ya sanar da haka a cikin wata takarda mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2024 waccw kuma take dauke da lamba kamar haka; COD/DIR/INT/CIR/001/025.

ADVERTISEMENT

Wannan takardar, na daga cikin sake maimacin gargadin da Bankin na CBN ya fitar a ranar 13 ga watan Nuwumbar 2024

Kazalika, Bankin ya nuna bacin ransa kan yadda ake ci gaba da sayar da sabbin takardun kudaden

LABARAI MASU NASABA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Bankin na CBN ya ci gaba da cewa, sayar da sabbin takardun kudaden na janyo karancin sabbin kudaden a hannun alummar kasar.

CBN ya kara da cewa, wannan halin na sayar da sabbin takardun kudaden kasar, zai iya yiwa tattalin azrkin Nijeriya illa da kuma zubar da kimar kasar tsarin kula da kudaden kasar.

Takardar ta sanar da cewa, Bankin na CBN ya kara zage damtse wajen bibiyar ayyukan da ake gudanar a cikin Bankunan kasar da kuma a wajen injinan cire kudi na ATM, domin duba yawan kudaden da abokan hudda da bankuna suka cire, musamman domin a bankado da irin wadannan mutanen masu sayar da sabbin takardun kudaden, a daukacin fadin Nijeriya.

A cewar takardar, duk Bankin da da Babban Bankin na CBN ya kama da aikta wannan harkallar, za a hukunta shi ciki har da cin su tarar kudi ta Naira miliyan 150.

Bankin ya ci gaba da cewa, akwai doka ta(BOFIA) 2020 da aka tanada domin hukunta duk wanda aka kama yana aikata wannan harkallar.

Wani jami’i a Bankin na CBN da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya sanar da cewa, wannan matakin da Bankin ya yanke na hukunta duk wanda aka kama yana yin wannan harkallar, za ta dakushe kwarin guiwar masu sayar da sabbin takardun kudaden kasar.

A cewarsa, mun mayar da hankali wajen ganin ana bai wa tkardun kudin kasar kimar da suke da ita.

A bisa haka ne, Babban Bankin ya umarci daukacin Bankunan kasar da sauran cibiyoyin hada-hadar kudade da su tabbatar da ana bin ka’ida hada-hadar kudade a rassan su.

A cewar Babban Bankin na CBN, wadannan matakan na da matukar mahimmanci, musamman domin a samu takardun kudaden, suna zagayawa a hanun jama’a yadda ya kamata.

Kazalika, wani ma’aikacin banki da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya tabbatar da wannan umarnin da Bankin na CBN, ya umarci Bankunan da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.

Ya yabawa Bankin na CBN, bisa daukar wannan matakan, inda ya bayyana cewa, akwai kuma bukatar Bankunan kasar, su goyi bayan matakan na Bankin CBN.

Wannan makain na Bankin CBN na daya daga cikin matakan Bankin na kokarin tsarkake gudanar da ayyukan Bankunan kasar da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
Tattalin Arziki

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno

Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno

November 18, 2025
Bukatar Samar Da Cikkakken Tsaro Ga Hukumar Zabe

’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

November 18, 2025
Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.