• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
6 months ago
in Tattalin Arziki
0
tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da cewa, zai kakabawa Bakununan Kasuwanci na kasar tarar Naira miliyan 150, idan aka same su suna taimakawa wajen sayar da sabbin takardun kudade.

Kazalika, Bankin na CBN, ya kuma sanar da cewa, zai hukunta ‘yan koren wadannan bankunan da ke sayar da sabbin takardun kudin.

  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC
  • Wolves Ta Naɗa Vitor Pereira A Matsayin Sabon Kocinta

Mukaddashin riko na sashen gudanar da ayyuka na Bankin Solaja Mohammed J. ya sanar da haka a cikin wata takarda mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2024 waccw kuma take dauke da lamba kamar haka; COD/DIR/INT/CIR/001/025.

Wannan takardar, na daga cikin sake maimacin gargadin da Bankin na CBN ya fitar a ranar 13 ga watan Nuwumbar 2024

Kazalika, Bankin ya nuna bacin ransa kan yadda ake ci gaba da sayar da sabbin takardun kudaden

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Bankin na CBN ya ci gaba da cewa, sayar da sabbin takardun kudaden na janyo karancin sabbin kudaden a hannun alummar kasar.

CBN ya kara da cewa, wannan halin na sayar da sabbin takardun kudaden kasar, zai iya yiwa tattalin azrkin Nijeriya illa da kuma zubar da kimar kasar tsarin kula da kudaden kasar.

Takardar ta sanar da cewa, Bankin na CBN ya kara zage damtse wajen bibiyar ayyukan da ake gudanar a cikin Bankunan kasar da kuma a wajen injinan cire kudi na ATM, domin duba yawan kudaden da abokan hudda da bankuna suka cire, musamman domin a bankado da irin wadannan mutanen masu sayar da sabbin takardun kudaden, a daukacin fadin Nijeriya.

A cewar takardar, duk Bankin da da Babban Bankin na CBN ya kama da aikta wannan harkallar, za a hukunta shi ciki har da cin su tarar kudi ta Naira miliyan 150.

Bankin ya ci gaba da cewa, akwai doka ta(BOFIA) 2020 da aka tanada domin hukunta duk wanda aka kama yana aikata wannan harkallar.

Wani jami’i a Bankin na CBN da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya sanar da cewa, wannan matakin da Bankin ya yanke na hukunta duk wanda aka kama yana yin wannan harkallar, za ta dakushe kwarin guiwar masu sayar da sabbin takardun kudaden kasar.

A cewarsa, mun mayar da hankali wajen ganin ana bai wa tkardun kudin kasar kimar da suke da ita.

A bisa haka ne, Babban Bankin ya umarci daukacin Bankunan kasar da sauran cibiyoyin hada-hadar kudade da su tabbatar da ana bin ka’ida hada-hadar kudade a rassan su.

A cewar Babban Bankin na CBN, wadannan matakan na da matukar mahimmanci, musamman domin a samu takardun kudaden, suna zagayawa a hanun jama’a yadda ya kamata.

Kazalika, wani ma’aikacin banki da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya tabbatar da wannan umarnin da Bankin na CBN, ya umarci Bankunan da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.

Ya yabawa Bankin na CBN, bisa daukar wannan matakan, inda ya bayyana cewa, akwai kuma bukatar Bankunan kasar, su goyi bayan matakan na Bankin CBN.

Wannan makain na Bankin CBN na daya daga cikin matakan Bankin na kokarin tsarkake gudanar da ayyukan Bankunan kasar da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

Next Post

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

Related

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

3 days ago
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

3 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 month ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

LABARAI MASU NASABA

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.