• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
7 months ago
in Tattalin Arziki
0
tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da cewa, zai kakabawa Bakununan Kasuwanci na kasar tarar Naira miliyan 150, idan aka same su suna taimakawa wajen sayar da sabbin takardun kudade.

Kazalika, Bankin na CBN, ya kuma sanar da cewa, zai hukunta ‘yan koren wadannan bankunan da ke sayar da sabbin takardun kudin.

  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC
  • Wolves Ta Naɗa Vitor Pereira A Matsayin Sabon Kocinta

Mukaddashin riko na sashen gudanar da ayyuka na Bankin Solaja Mohammed J. ya sanar da haka a cikin wata takarda mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2024 waccw kuma take dauke da lamba kamar haka; COD/DIR/INT/CIR/001/025.

Wannan takardar, na daga cikin sake maimacin gargadin da Bankin na CBN ya fitar a ranar 13 ga watan Nuwumbar 2024

Kazalika, Bankin ya nuna bacin ransa kan yadda ake ci gaba da sayar da sabbin takardun kudaden

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Bankin na CBN ya ci gaba da cewa, sayar da sabbin takardun kudaden na janyo karancin sabbin kudaden a hannun alummar kasar.

CBN ya kara da cewa, wannan halin na sayar da sabbin takardun kudaden kasar, zai iya yiwa tattalin azrkin Nijeriya illa da kuma zubar da kimar kasar tsarin kula da kudaden kasar.

Takardar ta sanar da cewa, Bankin na CBN ya kara zage damtse wajen bibiyar ayyukan da ake gudanar a cikin Bankunan kasar da kuma a wajen injinan cire kudi na ATM, domin duba yawan kudaden da abokan hudda da bankuna suka cire, musamman domin a bankado da irin wadannan mutanen masu sayar da sabbin takardun kudaden, a daukacin fadin Nijeriya.

A cewar takardar, duk Bankin da da Babban Bankin na CBN ya kama da aikta wannan harkallar, za a hukunta shi ciki har da cin su tarar kudi ta Naira miliyan 150.

Bankin ya ci gaba da cewa, akwai doka ta(BOFIA) 2020 da aka tanada domin hukunta duk wanda aka kama yana aikata wannan harkallar.

Wani jami’i a Bankin na CBN da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya sanar da cewa, wannan matakin da Bankin ya yanke na hukunta duk wanda aka kama yana yin wannan harkallar, za ta dakushe kwarin guiwar masu sayar da sabbin takardun kudaden kasar.

A cewarsa, mun mayar da hankali wajen ganin ana bai wa tkardun kudin kasar kimar da suke da ita.

A bisa haka ne, Babban Bankin ya umarci daukacin Bankunan kasar da sauran cibiyoyin hada-hadar kudade da su tabbatar da ana bin ka’ida hada-hadar kudade a rassan su.

A cewar Babban Bankin na CBN, wadannan matakan na da matukar mahimmanci, musamman domin a samu takardun kudaden, suna zagayawa a hanun jama’a yadda ya kamata.

Kazalika, wani ma’aikacin banki da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya tabbatar da wannan umarnin da Bankin na CBN, ya umarci Bankunan da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.

Ya yabawa Bankin na CBN, bisa daukar wannan matakan, inda ya bayyana cewa, akwai kuma bukatar Bankunan kasar, su goyi bayan matakan na Bankin CBN.

Wannan makain na Bankin CBN na daya daga cikin matakan Bankin na kokarin tsarkake gudanar da ayyukan Bankunan kasar da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

Next Post

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

Related

Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

5 days ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

1 week ago
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Tattalin Arziki

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

2 weeks ago
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
Tattalin Arziki

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

2 weeks ago
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

3 weeks ago
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
Tattalin Arziki

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

3 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

LABARAI MASU NASABA

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

July 23, 2025
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

July 23, 2025
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

July 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

July 23, 2025
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

July 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

July 23, 2025
Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.