• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
9 months ago
in Tattalin Arziki
0
tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sanar da cewa, zai kakabawa Bakununan Kasuwanci na kasar tarar Naira miliyan 150, idan aka same su suna taimakawa wajen sayar da sabbin takardun kudade.

Kazalika, Bankin na CBN, ya kuma sanar da cewa, zai hukunta ‘yan koren wadannan bankunan da ke sayar da sabbin takardun kudin.

  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC
  • Wolves Ta Naɗa Vitor Pereira A Matsayin Sabon Kocinta

Mukaddashin riko na sashen gudanar da ayyuka na Bankin Solaja Mohammed J. ya sanar da haka a cikin wata takarda mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2024 waccw kuma take dauke da lamba kamar haka; COD/DIR/INT/CIR/001/025.

Wannan takardar, na daga cikin sake maimacin gargadin da Bankin na CBN ya fitar a ranar 13 ga watan Nuwumbar 2024

Kazalika, Bankin ya nuna bacin ransa kan yadda ake ci gaba da sayar da sabbin takardun kudaden

Labarai Masu Nasaba

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Bankin na CBN ya ci gaba da cewa, sayar da sabbin takardun kudaden na janyo karancin sabbin kudaden a hannun alummar kasar.

CBN ya kara da cewa, wannan halin na sayar da sabbin takardun kudaden kasar, zai iya yiwa tattalin azrkin Nijeriya illa da kuma zubar da kimar kasar tsarin kula da kudaden kasar.

Takardar ta sanar da cewa, Bankin na CBN ya kara zage damtse wajen bibiyar ayyukan da ake gudanar a cikin Bankunan kasar da kuma a wajen injinan cire kudi na ATM, domin duba yawan kudaden da abokan hudda da bankuna suka cire, musamman domin a bankado da irin wadannan mutanen masu sayar da sabbin takardun kudaden, a daukacin fadin Nijeriya.

A cewar takardar, duk Bankin da da Babban Bankin na CBN ya kama da aikta wannan harkallar, za a hukunta shi ciki har da cin su tarar kudi ta Naira miliyan 150.

Bankin ya ci gaba da cewa, akwai doka ta(BOFIA) 2020 da aka tanada domin hukunta duk wanda aka kama yana aikata wannan harkallar.

Wani jami’i a Bankin na CBN da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya sanar da cewa, wannan matakin da Bankin ya yanke na hukunta duk wanda aka kama yana yin wannan harkallar, za ta dakushe kwarin guiwar masu sayar da sabbin takardun kudaden kasar.

A cewarsa, mun mayar da hankali wajen ganin ana bai wa tkardun kudin kasar kimar da suke da ita.

A bisa haka ne, Babban Bankin ya umarci daukacin Bankunan kasar da sauran cibiyoyin hada-hadar kudade da su tabbatar da ana bin ka’ida hada-hadar kudade a rassan su.

A cewar Babban Bankin na CBN, wadannan matakan na da matukar mahimmanci, musamman domin a samu takardun kudaden, suna zagayawa a hanun jama’a yadda ya kamata.

Kazalika, wani ma’aikacin banki da bai bukaci a bayyana sunan sa ba, ya tabbatar da wannan umarnin da Bankin na CBN, ya umarci Bankunan da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.

Ya yabawa Bankin na CBN, bisa daukar wannan matakan, inda ya bayyana cewa, akwai kuma bukatar Bankunan kasar, su goyi bayan matakan na Bankin CBN.

Wannan makain na Bankin CBN na daya daga cikin matakan Bankin na kokarin tsarkake gudanar da ayyukan Bankunan kasar da kuma cibiyoyin hada-hadar kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

Next Post

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

Related

tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

7 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

7 days ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

1 week ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

2 weeks ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Bukaci A Kare Kasashe 26 Daga Fadawa Talauci A 2050

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.