• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa alkaluman bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na shekarun baya bayan nan, da shaidun zahiri dake fitowa daga sassan hukumomin kasa da kasa, muna iya ganin yadda tattalin arzikin kasar Sin ya zamo muhimmin karfi dake ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya, matakin dake amfanar al’ummun kasar ta Sin, yake kuma yin tasiri mai kyau ga sauran sassan kasa da kasa.

Idan mun waiwayi baya, muna iya tuna irin gudummawar da kasar Sin ta baiwa duniya, yayin da ake shan fama da annobar COVID-19, ta hanyar samar da gudummawar kayayyakin yaki da cutar, da rigakafi, kana Sin ta aiwatar da matakan wanzar da safarar hajojin bukatar yau da kullum zuwa dukkanin sassan duniya, musamman a gabar da kamfanoni da dama a sauran sassan duniya suka gaza sauke wannan nauyi.

  • Taruka Biyu Na Sin Sun Bayyana Yadda Kasar Ke More Damar Ci Gaba Tare Da Kasashe Daban Daban
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mata 7 A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Kajuru

Masharhanta na ganin wadannan nasarori, da gudummawa da Sin ta baiwa duniya, ba kawai sun faru ne hakan ba, hasali ma hakan sakamako ne na aiwatar da kyawawan manufofi masu karko, karkashin hadin gwiwar gwamnati da bangaren al’ummun kasar da suka dukufa wajen aiki tukuru.

Ana iya ganin yadda Sin ke kara karfafa hadin gwiwar raya tattalin arziki, da cinikayya, tare da sauran sassan kasashen duniya, yayin da a hannu guda take daidaita tsara ayyukan cudanya tsakaninta da sauran rukunonin samar da ci gaba na duniya. Kaza lika, Sin ta yi fice wajen bunkasa zuba jari, da bude kasuwanninta ga sassan kasa da kasa.

A ganin kwararru, salon samar da ci gaba mai inganci da Sin ke aiwatarwa, da yaukaka hadin gwiwarta da sauran sassa, musamman ma kasashe masu tasowa, ya haifar da tarin alherai na cimma moriyar juna.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Karkashin manufofi daban daban na inganta hadin gwiwa, Sin ta zamo cibiyar raya harkokin tattalin arziki da zuba jari ta duniya, kana manufofinta na raya tattalin arziki sun yi tasirin gaske a fannin yaki da fatara, da aza tubulin gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama, aikin da masharhanta da dama ke ganin kyakkyawan misali ne, kuma darashi da ya kamata sauran sassan duniya su yi koyi da shi. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Next Post

Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

7 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

9 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

10 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

11 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

12 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

14 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.