• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Kasar sin

Bisa alkaluman bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na shekarun baya bayan nan, da shaidun zahiri dake fitowa daga sassan hukumomin kasa da kasa, muna iya ganin yadda tattalin arzikin kasar Sin ya zamo muhimmin karfi dake ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya, matakin dake amfanar al’ummun kasar ta Sin, yake kuma yin tasiri mai kyau ga sauran sassan kasa da kasa.

Idan mun waiwayi baya, muna iya tuna irin gudummawar da kasar Sin ta baiwa duniya, yayin da ake shan fama da annobar COVID-19, ta hanyar samar da gudummawar kayayyakin yaki da cutar, da rigakafi, kana Sin ta aiwatar da matakan wanzar da safarar hajojin bukatar yau da kullum zuwa dukkanin sassan duniya, musamman a gabar da kamfanoni da dama a sauran sassan duniya suka gaza sauke wannan nauyi.

  • Taruka Biyu Na Sin Sun Bayyana Yadda Kasar Ke More Damar Ci Gaba Tare Da Kasashe Daban Daban
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mata 7 A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Kajuru

Masharhanta na ganin wadannan nasarori, da gudummawa da Sin ta baiwa duniya, ba kawai sun faru ne hakan ba, hasali ma hakan sakamako ne na aiwatar da kyawawan manufofi masu karko, karkashin hadin gwiwar gwamnati da bangaren al’ummun kasar da suka dukufa wajen aiki tukuru.

Ana iya ganin yadda Sin ke kara karfafa hadin gwiwar raya tattalin arziki, da cinikayya, tare da sauran sassan kasashen duniya, yayin da a hannu guda take daidaita tsara ayyukan cudanya tsakaninta da sauran rukunonin samar da ci gaba na duniya. Kaza lika, Sin ta yi fice wajen bunkasa zuba jari, da bude kasuwanninta ga sassan kasa da kasa.

A ganin kwararru, salon samar da ci gaba mai inganci da Sin ke aiwatarwa, da yaukaka hadin gwiwarta da sauran sassa, musamman ma kasashe masu tasowa, ya haifar da tarin alherai na cimma moriyar juna.

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Karkashin manufofi daban daban na inganta hadin gwiwa, Sin ta zamo cibiyar raya harkokin tattalin arziki da zuba jari ta duniya, kana manufofinta na raya tattalin arziki sun yi tasirin gaske a fannin yaki da fatara, da aza tubulin gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil adama, aikin da masharhanta da dama ke ganin kyakkyawan misali ne, kuma darashi da ya kamata sauran sassan duniya su yi koyi da shi. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.