• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
Sin

Jimilar jami’an kasashe 45 abokan huldar kasar Sin karkashin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika (FOCAC) da na kungiyar Tarayyar Afrika (AU), sun fara karbar horon dake mayar da hankali kan yaki da talauci, wanda ke gudana a jihar Ningxia ta kabilar Hui mai cin gashin kanta daga ranar 19 zuwa 26 ga watan Oktoba.

Bayanai sun nuna cewa, nahiyar Afrika ce mafi fama da talauci a duniya, inda kasashe 23 cikin 28 mafiya talauci ke nahiyar, lamarin da ya sa ta mamaye sama da kaso 30 cikin dari na adadin masu fama da talauci na duniya. A daya hannu kuma, kasar Sin ce wadda ta gabatarwa duniya wani abun al’ajabi na yaki da talauci, inda ta fatattaki talauci baki daya, shekaru 10 kafin lokacin da MDD ta tsara na ganin bayan talauci.

To a matsayinsu na abokan hulda na kut da kut, tabbas kasashen Afrika ba su da inda za su koyi dabarun raya kansu, ciki har da yaki da talauci, face wajen kasar Sin, saboda gogewa da jajircewarta da kuma yadda ta zama misali ga daukacin duniya.

Jihar Ningxia na daya daga cikin wuraren da Sin ta fafata yaki da takauci inda dukkan kauyukan jihar 1,100 suka yi adabo da talauci. Horon jami’an wanda ya kunshi lakcoci da ziyarce-ziyarce, zai ba su damar gani da idanunsu da tantance irin ayyuka da sadaukarwar da Sin ta yi domin fitar da al’ummarta daga talauci. A ko da yaushe, muna ganin yadda ake alakanta yawan jama’a da gazawar manufofin gwamnatoci na samun sakamakon raya kasa ko yaki da talauci, sai dai, kasar Sin ta nuna cewa, batun ba haka yake ba, wato yawan al’umma ba dalili ne na rashin ci gaba ba. Baya ga haka, kasar Sin ba ta fita ta yi mamaya ko cin zali ko mulkin mallaka ba, kafin kai wa matsayin da ta kai, don haka, babu dalilin cewa rashin karfi ne ya kawo tasgaro ga samun ci gaba. A ganina babban batu shi ne, yadda jami’an nan za su fahimci cewa, kasar Sin dogaro ta yi da mutanenta da ilimi da kwarewarsu da albarkatun da take da shi wajen yakar talauci. Ni ganau ce, domin na je Ningxia, na ga yadda mata suka yaki talauci ta hanyar mayar da ciyawa tsintsiya, da aiwatar da kirkire-kirkire da dama da sauran wasu dabaru. Ba Ningxia kadai ba, dukkan sassan kasar Sin kan yi amfani da duk albarkar da suke da ita wajen mayar ita mai daraja domin kyautata rayuwarsu.

Fatan ita ce, bayan komawa gida wadannan jami’ai su aiwatar da abun da suka koya domin babban kashin bayan ci gaban Sin shi ne, kyakkyawan kudurin shugabanci. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?
Daga Birnin Sin

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Next Post
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.