ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
CIIE

A ranar jiya aka rufe bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin wato CIIE karo na 8, inda aka cimma yarjejeniyoyin ciniki da aka kiyasta kudinsu ya kai dala biliyan 83.49 a cikin shekara guda, adadin da ya karu da kashi 4.4 cikin 100 idan aka kwatanta da na bikin bara, wanda ya zama mafi girma a tarihi. Don fadada bude kasuwa ga kasashe mafi karancin ci gaba, bikin na wannan karo ya kara fadada sassan da ke baje kolin kayayyakin Afirka, don tallafawa kasashen Afirka dake da huldar diflomasiyya da Sin wajen amfani da manufar cire haraji akan dukannin kayayyakinsu da suke fitarwa zuwa kasar Sin, har ma adadin kamfanonin Afirka da suka halarci bikin ya karu da kashi 80 cikin 100 idan aka kwatanta da na bara.

 

Rwanda kasa ce mai yawan noman barkono, amma saboda karancin bukatu a cikin gidanta, barkonon Rwanda ya taba fuskantar matsalar rashin samun kasuwanni. A CIIE karo na farko, miyar barkono ta Rwanda ta samu matukar karbuwa a kasuwar Sin saboda dandanonta na musamman. A watan Maris na 2021, gwamnatocin Sin da Rwanda sun sanya hannu kan yarjejeniya game da busasshen barkono na Rwanda da ake shigowa da su Sin, inda Rwanda ta zama kasar Afirka ta farko da ta fara fitar da busasshen barkono zuwa Sin. Bisa ga yarjejeniyar, kafin shekara ta 2026, masu sayar da barkono na Rwanda za su fitar da tan 50,000 na busasshen barkono zuwa Sin. A yau, noman barkono ya zama muhimmiyar sana’ar samar da kudi a Rwanda, kuma ya haifar da bunkasuwar sana’o’i masu alaka, lamarin da ya samar da karin ayyukan yi ga mutanen yankin. Jakadan Rwanda a Sin James Kimonyo ya ce, “CIIE ya zama dandali mai muhimmanci ga Rwanda don baje kolin ingantattun kayayyakinta. Za mu ci gaba da baje kolin kayayyakinmu iri-iri, mu yi amfani da wadannan budaddun dandamali, mu fitar da karin ingantattun kayayyakin Rwanda zuwa kasuwar Sin.”

ADVERTISEMENT

 

Daga daukar akwati don gabatar da kayayyaki, zuwa yanzu da ake fitar da kayayyaki ta hanyar kwantena, kasashen Afirka kamar Rwanda sun samu damar habaka cinikinsu ta hanyar nuna ingantattun kayayyakinsu na noma a wannan budadden dandali wato CIIE.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

 

Mun yi imanin cewa a nan gaba, karin kamfanonin Afirka za su ga fa’idar budaddiyyar kasuwar Sin ta CIIE, za su kuma kara zurfafa hadin gwiwa tare da Sin, da yin amfani da damammakin CIIE don samun moriyar juna. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
Next Post
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, 'Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.