• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Ya Tabbatar Da Matsayin Kasar Sin A Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
CIIE Ya Tabbatar Da Matsayin Kasar Sin A Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na bakwai, da za a gudanar daga ranar 5 zuwa 10 ga watan Nuwamba, shaida ce na amincewa da karuwar karfin tattalin arzikin kasar Sin, da muhimmiyar rawar da take takawa wajen raya dukkan fannonin tattalin arzikin duniya tun daga hada-hadar hajojin gargajiya zuwa sabbin fasahohin da suka kasance ginshikin ci gaban tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba. 

 

Yadda shugabannin kasashen waje da dama suka bayyana ra’ayin halartar bikin bude baje kolin da ma yadda masu baje koli daga kasashen waje suka nemi damar samun sararin baje hajojinsu, wata shaida ce ta bunkasar dangantakar cinikayya, da ta tabbatar da kasar Sin a matsayin kasuwa mai girma. Hakazalika, kasashen Norway, Slovakia, Benin, Burundi da Madagaskar, da kuma asusun bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya, za su halarci baje kolin na CIIE a karo na farko, wannan ya kara tabbatar da muhimmancin da kasuwar kasar Sin ke da shi ga tattalin arzikin duniya.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Kan AI
  • Dalilin Da Yasa Kaduna Ke Kan Gaba A Samar Da Kuɗaɗen Shiga A Arewa – Shugaban KADIRS

Kana kasashen ketare sun kuduri aniyar nuna yadda suke cudanya da kasar Sin, da kuma yadda Sin ke da muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikinsu da kudurin fadada bunkasa tattalin arzikin duniya ba tare da gurbata muhalli ba. Da a ce kasar Sin ba ta shiga sha’anin tattalin arzikin duniya ana damawa da ita ba, to da wadatar cinikayya tsakanin kasa da kasa ta fuskanci barazana. Kuma kamar yadda sunan ya tabbatar, babban makasudin baje kolin CIIE shi ne ya zama wurin tuntuba ga kamfanonin da ke da sha’awar kara mu’amalar cinikayya da kasar Sin, da kuma samun abokan huldar kasuwanci na kasar Sin da ke son shigo da kayayyaki ko hidimomi.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Ta hanyar turjewa takunkumi da sauran manufofin kasashen yammacin duniya da ke inganta kariyar cinikayya, baje kolin CIIE ya kasance kofar da duniya ke bi wajen shiga kasar Sin, saboda masu baje kolin sun san cewa, ci gaban tattalin arzikin duniya ya ta’allaka ne ga yin cinikayya cikin ‘yanci tare da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙungiyar Likitoci Ta Buƙaci Dakatar Da Kwamishina Kan Zargin Cin Zarafin Likita A Kano

Next Post

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

6 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

8 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

9 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

10 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

11 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

13 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.