• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE: ‘Yan Kasuwan Kasa Da Kasa Na Alla-alla Wajen Yin Amfani Da Damar Ci Gaban Kasar Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
CIIE: ‘Yan Kasuwan Kasa Da Kasa Na Alla-alla Wajen Yin Amfani Da Damar Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a gudanar da taron baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin CIIE karo na 6 daga ranar 5 zuwa 10 ga wata a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin. A yau Jumma’a ne aka kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da taron. Baki daga kasashe, yankuna da hukumomin kasa da kasa guda 154 da kamfanoni fiye da 3400 na duniya za su halarci taron cikin kwanaki da dama masu zuwa, ciki had da kamfanoni masu alaka da raya shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” sama da 1500. Abin da kamata a lura da shi, shi ne a cikin wadannan kamfanoni fiye da 3400, wasu da dama sun halarci taron na CIIE sau 6 baki daya. 

Mene ne dalilin hakan? Saboda halartar taron na CIIE ya ba su damar samun bunkasuwa. Kayayyakin da suke baje koli a taron CIIE sun zama hajojin da suke sayarwa a kasar Sin, kana suna zuba jari a kasar Sin a maimakon halartar taron na CIIE kawai. Tun tuni kasar Sin ta yi alkawarin mayar da kasuwar Sin zuwa kasuwar duniya mai kunshe da kowa. Ta kuma cika alkawarinta a zahiri. Ta yi ta ba kamfanonin kasa da kasa damarmakin samun ci gaba.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Alkaluman tattalin arzikin kasar Sin na watanni 9 na farkon bana kuma sun tabbatar da haka. Karuwar tattalin arzikin kasar Sin wato GDP ta kai kaso 5.2 a watanni 9 na farkon bana bisa makamancin lokaci na shekarar bara, karuwar ta fi ta rukunonin duniya masu karfin tattalin arziki. Ciki kuma karuwar yin sayayya ta fi jan hankali, wadda ta taimakawa karuwar GDP har kaso 4.4. Wadannan alkaluma sun samar da kamfanoni masu jarin waje kyawawan damarmaki.

Baya ga dimbin al’umma mai yawan biliyan 1.4 da kuma masu matsakaitan kudin shiga sama da miliyan 400, gwamnatin kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan bude kofa ga kasashen ketare, lamarin da ya jawo hankalin kamfanoni masu jarin waje da dama, musamman ma shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ke kokarin aiwatarwa cikin hadin gwiwar kasa da kasa, tana amfanawa kasashen duniya sosai. A sashen nune-nunen kasa da kasa a taron CIIE na wannan karo, akwai kasashe 64 da suke raya shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” daga cikin dukkan kasashen 72. A ‘yan kwanakin baya, jiragen kasa da ke tafiya tsakanin kasar Sin da kasashen Turai suna ta jigilar kayayyakin kasashen da ke raya shawarar zuwa taron CIIE.

Har ila yau taron na CIIE na bai wa daukacin kasashen duniya damar samun ci gaba, musamman ma taimakawa kasashe masu rauni samun bunkasuwa, lamarin da ya burge wasu kamfanoni. Kasashe mafiya karancin ci gaba, wadanda suke raya shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” sun samu wurin nune-nune ba tare da biyan kudi ba a taron na CIIE, tare da samun kudin tallafin yin nune-nune da haraji mai gatanci kan kayayyakin da za su nuna, ta yadda kayayyakinsu masu halin musamman za su samu damar shiga kasuwar kasar Sin

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kokarin da kasar Sin take bayarwa ya shaida cewa, manufar kasar Sin ta shirya taron na CIIE ita ce kara azama kan gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkan bil Adama. Taron na CIIE ya sanya kasashen duniya sun kara sanin aniyar kasar Sin ta bin manufar cudanyar sassa daban daban da samar wa kasashen duniya damar ci gaba, da kuma matakan da take dauka. Da ma wasu daga kasashen yamma sun yi shelar cewa, masu jarin waje sun janye jiki daga kasar Sin, amma yadda kamfanoni masu jarin waje suke halartar taron CIIE sau da dama, ya sanya gaskiya za ta yi halin ta.

Hukumar kara azama kan cinikayya ta kasar Sin ta kaddamar da rahoto a kwanan baya cewa, kamfanoni masu jarin waje da aka yi musu tambaya wadanda yawansu ya wuce kaso 80, sun gamsu da yanayin kasuwancin kasar Sin. Ya zuwa yanzu kasuwar kasar Sin na jan hankalinsu sosai. Bude taron na CIIE karo na 6 za ta kara nuna yadda ake yin amfani da damar da kasar Sin ke samarwa. (Tasallah Yuan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Kare Lafiya Lokacin Hunturu – Dakta Sufyan 

Next Post

Ina Da Kwarewar Shugabancin Majalisa Fiye Da Akpabio – Ndume

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

8 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

9 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

10 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

11 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

12 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

23 hours ago
Next Post
Ina Da Kwarewar Shugabancin Majalisa Fiye Da Akpabio – Ndume

Ina Da Kwarewar Shugabancin Majalisa Fiye Da Akpabio – Ndume

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.