Kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC, ta kuduri aniyar gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a fadin kasar baki daya domin nuna rashin amincewa da cire tallafin man fetur a ranar Laraba, yayin da ta bayyana shakku kan yadda shugaba Bola Tinubu zai iya shawo kan hauhawar farashin kayayyaki da hauhawar farashin man fetur.
A wani taro da Kwamitin Gudanarwar Kwamiti kan raba tallafi a fadar Shugaban kasa da ke Abuja a ranar Litinin, Shugaban Kungiyar, Joe Ajaero, ya nanata cewa, ba gudu ba ja da baya, zanga-zangar lumana da ma’aikatan suka shirya yi a ranar Laraba tana nan.
Ya warware damuwar da ake da ita cewa, batagari ka iya shiga cikin zanga-zangar su haifar da matsalar tsaro, Ajaero ya tabbatar da cewa ba a taba samun tashin hankula ba a tarihin zanga-zangar ma’aikata.
Ajaero ya yi kira ga hukumomin tsaro da su tabbatar da tsaron lafiyar ma’aikatan yayin zanga-zangar.