• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Za Mu Ba Da Shawarar Karin Albashi Don Taimaka Wa ‘Yan Kasa – Gwamna Bala

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamna Bala

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya ce, kwamitin da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC) ta kafa da aka dora wa alhalin bayar da shawarorin hanyoyin da za a bi wajen raba wa al’ummar kasa tallafi da gudunmawa sakamakon radadin cire tallafin Mai da ake fuskanta, za su gudanar da aikinsu tukuru domin muradin ‘yan kasa baki daya.

Gwamna Bala wanda ke wakiltar shiyyar Arewa Maso Gabas a cikin kwamitin ya shaida hakan ne a lokacin da ke ganawa da ‘yan jarida a Bauchi.

  • Yadda Aka Yi Fito-na-fito Da Masu Gidaje Da Jami’an Rusau A Kano

A cewarsa, mambohin kwamitin wadanda suke karkashin jagorancin gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasiru Idris, za su tabbatar dukkanin ‘yan kasa sun samu tallafi a kowani bangare domin rage musu radadi halin da aka tsinci kai sakamakon cire tallafin Mai ba tare da la’akari da banbancin jam’iyyar ba.

Ya ce, “Dukka da Gwamnonin da suke bangaren adawa da na gwamnati mai ci ta APC sun fahimci yunkurin da gwamnatin tarayya ta dauka bisa dacewa, don haka akwai tabbacin ba za a siyasantar da yunkurin ba.”

A cewarsa, NEC da wakilan kungiyoyin kwadago sun fahimci alfanu da kalubalen da ke tattare da cire tallafin Mai, da hakan ya janyo wa al’ummar kasa musamman talakawa shiga matsatsi da kuncin rayuwa, don haka da bukatar a samar da tallafi mai ma’ana domin rage radadin.

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kan hanyoyin da ke da bukatar agajin gaggawa kuwa, Gwamma Bala Muhammad, ya ce kwamitin zai ba da shawarar karin albashi ga ma’aikata da kuma samar da tallafi ga al’ummar kasa, samar da motocin bas-bas domin rage wa jama’a wahalar sufuri da kawo shirye-shiryen masu fa’ida da al’ummar za su amfana.

Ya ce, kwamitin za su gabatar da rahoton su nan da sati biyu ga Majalisar Tattalin Arzikin Kasa domin daukar matakai na gaba.

Ya nemi al’ummar kasa da su kara hakuri kan halin da suke ciki, da fatan Gwamnatin tarayya za ta tabbatar da yin amfani da shawarorin da za su bayar domin rage wa jama’a wahala da radadi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Next Post
Duk Maniyyatan Da Muka Yi Wa Biza Sai Sun Sauke Farali Da Yardar Allah – NAHCON

Duk Maniyyatan Da Muka Yi Wa Biza Sai Sun Sauke Farali Da Yardar Allah – NAHCON

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.