• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda, ta zama Sakatariyar Gamayyar Ƙungiyar Matan Shugabannin Nijeriya Masu Fafutukar Yaƙi da Cutar Daji (FLAC).

 

Ƙungiyar tana faɗi-tashi wajen yaƙi da cutar kansa ta ta hanyar wayar da kai, tsara manufofi da kuma shiga tsakani kai-tsaye ga al’umma.

  • Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana
  • Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Naɗin nata ya nuna matuƙar jajircewa da irin gudunmawar da ta bayar wajen habaka kiwon lafiya, musamman a fannin wayar da kan jama’a game da cutar daji, rigakafin cutar daji da kulawa da masu cutar a Jihar Zamfara da kewaye.

 

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

A cikin sabon aikinta na ƙasa, Hajiya Huriyya za ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ‘yan uwanta mata, matan shugabanni don bunƙasa wayar da kai da tattara kayan aiki don inganta tsarin kula da cutar daji musamman ga al’ummomin da ba su da ƙarfi.

 

Naɗin nata ya biyo bayan bikin bayar da tallafin cutar daji na FLAC da aka yi a gidan gwamnatin jihar Imo a Asokoro, Abuja, inda suka tattauna kan ƙarfafa ayyukan ceto da inganta yaƙin gano cutar da wuri a faɗin Nijeriya.

 

Ta hanyar ba da fifiko ga kiwon lafiya al’umma, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta bambanta da sauran mata, inda ayyukanta ke amfanar masu rauni kai-tsaye. A ƙarƙashin jagorancinta, Jihar Zamfara ta yi aikin tantance cutar kansar nono kyauta, da wayar da kan jama’a, da kuma ɗaukar cikakken nauyin yi wa masu fama da cutar daji fiye da 100 tiyata. Gudunmawar da ta bayar na Naira Miliyan 3.5 don kula da marasa lafiya masu fama da cutar kansa ya nuna tausayi da kuma yadda ta ke tunkarar ƙalubalen kiwon lafiyar jama’a.

 

A matsayinta na Sakatariyar FLAC, ana sa ran jagorancinta zai ƙara ci gaba ga ƙungiyar haɗin gwiwar ta ƙasa baki ɗaya, gami da ba da shawarwari ga manufofin kiwon lafiya da suka haɗa da ayyukan hidimta wa al’umma da kulawa da kiwon lafiya. Naɗin nata ya kuma nuna cewa Arewacin Nijeriya na da tasiri kan ayyukan kiwon lafiya gami da cutar kansa.

 

Taron da aka yi a Abuja ya nuna bayar da tallafin kuɗi ga manyan ƙungiyoyi biyu masu tallafawa cutar kansa da suka haɗa da Network of People Impacted by Cancer in Nigeria (NePICiN) da Health & Psychological Trust Center, wanda ƙara nuna aniyar FLAC na inganta rayuwar masu fama da cutar kansa da waɗanda suka warke.

 

Shugabar FLAC kuma Uwargidan Gwamnan Jihar Imo, Barista Chioma Hope Uzodimma, ta yaba da shirin a matsayin “babban jari a rayuwa, mutunta rayuwar al’umma da kuma daidaiton kiwon lafiya.”

 

Taron ya samu halartar wasu fitattun matan manya da suka haɗa da Lami Ahmadu Fintiri (Mataimakiyar Shugabar FLAC), Dr. Linda Ayade, Monica Ugwuanyi, Hajiya Zainab Nasir Idris, H.E. Agyin Kefas, da Hajiya Huriyya Dauda Lawal.

 

Jajircewar da Hajiya Hariyya ta yi a wannan ƙasa tamu ba wai kawai ya ƙara nuna irin himmarta ba ne wajen fafutukar kula da lafiya har ma ya ƙara ƙarfafa gwiwarta a jihar Zamfara wajen kawo sauyi kan harkokin kiwon lafiyar al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

Next Post

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

Related

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

14 minutes ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

1 hour ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

2 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

2 hours ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

6 hours ago
Next Post
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

LABARAI MASU NASABA

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

September 20, 2025
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

September 20, 2025
FLAC

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.