• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

by Sulaiman
3 months ago
FLAC

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda, ta zama Sakatariyar Gamayyar Ƙungiyar Matan Shugabannin Nijeriya Masu Fafutukar Yaƙi da Cutar Daji (FLAC).

 

Ƙungiyar tana faɗi-tashi wajen yaƙi da cutar kansa ta ta hanyar wayar da kai, tsara manufofi da kuma shiga tsakani kai-tsaye ga al’umma.

  • Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana
  • Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Naɗin nata ya nuna matuƙar jajircewa da irin gudunmawar da ta bayar wajen habaka kiwon lafiya, musamman a fannin wayar da kan jama’a game da cutar daji, rigakafin cutar daji da kulawa da masu cutar a Jihar Zamfara da kewaye.

 

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

A cikin sabon aikinta na ƙasa, Hajiya Huriyya za ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ‘yan uwanta mata, matan shugabanni don bunƙasa wayar da kai da tattara kayan aiki don inganta tsarin kula da cutar daji musamman ga al’ummomin da ba su da ƙarfi.

 

Naɗin nata ya biyo bayan bikin bayar da tallafin cutar daji na FLAC da aka yi a gidan gwamnatin jihar Imo a Asokoro, Abuja, inda suka tattauna kan ƙarfafa ayyukan ceto da inganta yaƙin gano cutar da wuri a faɗin Nijeriya.

 

Ta hanyar ba da fifiko ga kiwon lafiya al’umma, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ta bambanta da sauran mata, inda ayyukanta ke amfanar masu rauni kai-tsaye. A ƙarƙashin jagorancinta, Jihar Zamfara ta yi aikin tantance cutar kansar nono kyauta, da wayar da kan jama’a, da kuma ɗaukar cikakken nauyin yi wa masu fama da cutar daji fiye da 100 tiyata. Gudunmawar da ta bayar na Naira Miliyan 3.5 don kula da marasa lafiya masu fama da cutar kansa ya nuna tausayi da kuma yadda ta ke tunkarar ƙalubalen kiwon lafiyar jama’a.

 

A matsayinta na Sakatariyar FLAC, ana sa ran jagorancinta zai ƙara ci gaba ga ƙungiyar haɗin gwiwar ta ƙasa baki ɗaya, gami da ba da shawarwari ga manufofin kiwon lafiya da suka haɗa da ayyukan hidimta wa al’umma da kulawa da kiwon lafiya. Naɗin nata ya kuma nuna cewa Arewacin Nijeriya na da tasiri kan ayyukan kiwon lafiya gami da cutar kansa.

 

Taron da aka yi a Abuja ya nuna bayar da tallafin kuɗi ga manyan ƙungiyoyi biyu masu tallafawa cutar kansa da suka haɗa da Network of People Impacted by Cancer in Nigeria (NePICiN) da Health & Psychological Trust Center, wanda ƙara nuna aniyar FLAC na inganta rayuwar masu fama da cutar kansa da waɗanda suka warke.

 

Shugabar FLAC kuma Uwargidan Gwamnan Jihar Imo, Barista Chioma Hope Uzodimma, ta yaba da shirin a matsayin “babban jari a rayuwa, mutunta rayuwar al’umma da kuma daidaiton kiwon lafiya.”

 

Taron ya samu halartar wasu fitattun matan manya da suka haɗa da Lami Ahmadu Fintiri (Mataimakiyar Shugabar FLAC), Dr. Linda Ayade, Monica Ugwuanyi, Hajiya Zainab Nasir Idris, H.E. Agyin Kefas, da Hajiya Huriyya Dauda Lawal.

 

Jajircewar da Hajiya Hariyya ta yi a wannan ƙasa tamu ba wai kawai ya ƙara nuna irin himmarta ba ne wajen fafutukar kula da lafiya har ma ya ƙara ƙarfafa gwiwarta a jihar Zamfara wajen kawo sauyi kan harkokin kiwon lafiyar al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.