Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a dawo da babban daraktan gidan talabijin na Nijeriya (NTA), Salihu Abdullahi Dembos, wanda aka dakatar bayan wasu sauye-sauye da aka samu a shugabancin gidan.
Shugaba Tinubu ne ya nada Dembos a matsayin babban darakta na gidan talabijin a watan Oktoban 2023.
- Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya
- Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Amma a yanzu zai dawo ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ya kuma umarci da a maido da babban daraktan yada labarai, Mista Ayo Adewuyi ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku, wanda zai kare a shekarar 2027.
Shugaba Tinubu ne ya nada Adewuyi a shekarar 2024.