• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-Ɗumi: An Sake Naɗa Sanusi Lamido Sanusi A Matsayin Sarkin Kano

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Da Ɗumi-Ɗumi: An Sake Naɗa Sanusi Lamido Sanusi A Matsayin Sarkin Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata majiya mai tushe ta tabbatar wa da LEADERSHIP cewar an dawo da Sarki Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.

Wannan mataki na zuwa ne bayan da majalisar dokokin jihar, ta yi wa dokar da ta ƙirƙiro sabbin masarautu huɗu a lokacin tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, kwaskwarima tare da rushe su a yau.

  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro
  • Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano

Sai dai ba a sanar da sake nada Sanusi II a hukumance ba, amma majiyar ta shaida wa LEADERSHIP cewar za a sake nada shi a ranar Juma’a.

A cewar majiyar “Bayan zartar da dokar Sanusi ya dawo kan kujerarsa babu bukatar sanarwa, kawai gwamna ake jira ya tabbatar.”

Tun da farko tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ne, ya yi amfani da dokar wajen tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, Sarkin Kano na 14 a 2020.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

A yau ne dai majalisar dokokin Jihar Kano, ta amince gyaran dokar da ta samar da sabbin masarautu a jihar tare da rushe masarautun da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya kirkiro.

Wannan na zuwa ne bayan zama da majalisar ta yi a yau Alhamis tare da yin duba a kan dokar da ta kirkiro sabbin masarautun.

Zaman majalisar na yau, wanda shi ne zama na uku, majalisar ta amince da kundirin gyaran dokar ta kafa masarautun jihar guda biyar, wanda aka samar a karkashin gwamnatin tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Tun da fari gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya sanar da zai sanya hannu idan majalisar ta amince da gyaran dokar.

Shugaban masu rinjaye kuma wakilin mazabar Dala, Hussein Dala ne, ya gabatar da kudirin gyara dokar a yayin zaman majalisar na ranar Talata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGandujekanoMasarautuSanusi Lamido II
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Next Post

Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

Related

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

5 hours ago
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

9 hours ago
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

11 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

20 hours ago
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Manyan Labarai

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

2 days ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

3 days ago
Next Post
Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan 'Labarin LEADERSHIP' Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.