• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ya gana a jiya Litinin da babban mai bada shawara kan harkokin tsaro na kasar Japan, Takeo Akiba a nan birnin Beijing, inda suka amince da ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu a matakai daban daban.

 

Hakika bayan tankiya da takalar da aka gani daga bangaren Japan a baya-bayan nan, musamman game da batun zubar da dagwalon nukiliya cikin teku, irin wannan tattaunawa ta jiya, tana nuna alamun cewa, Japan na son gyara kuskuren da ta tafka a baya.

  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai
  • Kasar Sin Ta Daukaka Kara Zuwa WTO Game Da Hukuncin Karshe Kan Matakin EU Kan Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Tarihi bai taba nuna inda rikici ya haifar da zaman lafiya ba. Da alama sabon firaministan Japan Shigeru Ishiba, ya fahimci hakan, sannan ya san hakkin makwabtaka, kuma yana kuma son gyara kuskuren kasarsa da ma dangantakar da ta yi tsami tsakaninta da Sin.

 

Labarai Masu Nasaba

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Zuwa yanzu, na san kowa ya fahimci cewa, kasar Sin tana mayar da hankali ne kan kare kanta da muradunta da kuma neman sulhu cikin lumana maimakon tsokana da tankiya da fito-na-fito. Haka kuma, kullum a shirye take wajen ganin an hada hannu an wanzar da zaman lafiya a yankin da ma duniya baki daya. Kuma ba shakka idan Japan ta nemi zaman lafiya da Sin, to tabbas Sin tana maraba da hakan.

 

A baya, Japan ta yi biris da kuken al’ummarta da na makotanta, inda ta bari wasu kasashe daga wajen su na amfani da ita domin cimma wasu muradu na kashin kai da kokarin ta da rikici tsakanin Sin da kasashe makwabtanta. Amma idan har a yanzu Japan ta fahimci hakan ba hanya ce mai bullewa ba, to za a samu zaman lafiya da ci gaban da ake muradi, sannan wasu daga waje ba za su samu damar tsoma baki da haifar da rikici a yankin ba.

 

A wannan gaba da ake tattaunawa, ya kamata Japan ta girmama makwabtanta, ta kuma dauki korafinsu da muhimmanci domin samun fahimtar juna da kuma kyautata alakarta da su. Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, dangantakar bangarorin biyu na wata gaba mai muhimmanci, don haka, ya kamata Japan ta mutunta kudurinta kan batun Taiwan da kuma daukar Sin a matsayin makwabciya kuma abokiyar hulda maimakon barazana ko abokiyar adawa. Kyakkyawar dangantaka tsakanin bangarorin biyu, za ta taka muhimmiyar rawa ga ci gabansu da zamantakewar al’ummarsu da ma yankinsu baki daya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Boko Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Botswana

Next Post

Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

Related

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

26 minutes ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

19 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

20 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

21 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

22 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

23 hours ago
Next Post
Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

LABARAI MASU NASABA

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.