• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ya gana a jiya Litinin da babban mai bada shawara kan harkokin tsaro na kasar Japan, Takeo Akiba a nan birnin Beijing, inda suka amince da ci gaba da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu a matakai daban daban.

 

Hakika bayan tankiya da takalar da aka gani daga bangaren Japan a baya-bayan nan, musamman game da batun zubar da dagwalon nukiliya cikin teku, irin wannan tattaunawa ta jiya, tana nuna alamun cewa, Japan na son gyara kuskuren da ta tafka a baya.

  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai
  • Kasar Sin Ta Daukaka Kara Zuwa WTO Game Da Hukuncin Karshe Kan Matakin EU Kan Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin

Tarihi bai taba nuna inda rikici ya haifar da zaman lafiya ba. Da alama sabon firaministan Japan Shigeru Ishiba, ya fahimci hakan, sannan ya san hakkin makwabtaka, kuma yana kuma son gyara kuskuren kasarsa da ma dangantakar da ta yi tsami tsakaninta da Sin.

 

Labarai Masu Nasaba

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Zuwa yanzu, na san kowa ya fahimci cewa, kasar Sin tana mayar da hankali ne kan kare kanta da muradunta da kuma neman sulhu cikin lumana maimakon tsokana da tankiya da fito-na-fito. Haka kuma, kullum a shirye take wajen ganin an hada hannu an wanzar da zaman lafiya a yankin da ma duniya baki daya. Kuma ba shakka idan Japan ta nemi zaman lafiya da Sin, to tabbas Sin tana maraba da hakan.

 

A baya, Japan ta yi biris da kuken al’ummarta da na makotanta, inda ta bari wasu kasashe daga wajen su na amfani da ita domin cimma wasu muradu na kashin kai da kokarin ta da rikici tsakanin Sin da kasashe makwabtanta. Amma idan har a yanzu Japan ta fahimci hakan ba hanya ce mai bullewa ba, to za a samu zaman lafiya da ci gaban da ake muradi, sannan wasu daga waje ba za su samu damar tsoma baki da haifar da rikici a yankin ba.

 

A wannan gaba da ake tattaunawa, ya kamata Japan ta girmama makwabtanta, ta kuma dauki korafinsu da muhimmanci domin samun fahimtar juna da kuma kyautata alakarta da su. Kamar yadda Wang Yi ya bayyana, dangantakar bangarorin biyu na wata gaba mai muhimmanci, don haka, ya kamata Japan ta mutunta kudurinta kan batun Taiwan da kuma daukar Sin a matsayin makwabciya kuma abokiyar hulda maimakon barazana ko abokiyar adawa. Kyakkyawar dangantaka tsakanin bangarorin biyu, za ta taka muhimmiyar rawa ga ci gabansu da zamantakewar al’ummarsu da ma yankinsu baki daya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Boko Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Botswana

Next Post

Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

Related

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma
Daga Birnin Sin

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

30 minutes ago
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

3 hours ago
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 
Daga Birnin Sin

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

4 hours ago
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci
Daga Birnin Sin

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

6 hours ago
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

14 hours ago
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

16 hours ago
Next Post
Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

Real Madrid: Me Ke Faruwa Ne A Santiago?

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.