• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-dumi: Dalibai Mata 8 Da Aka Sace A Kaduna Sun Tsere Daga Sansanin ‘yan ta’adda

El-Rufai ya yabawa daliban bisa jajircewa

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Da Dumi-dumi: Dalibai Mata 8 Da Aka Sace A Kaduna Sun Tsere Daga Sansanin ‘yan ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dalibai mata takwas da aka yi garkuwa da su a Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Awon a karamar hukumar Kachia a Jihar Kaduna, sun tsere daga sansanin ‘yan ta’addan.

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da daliban ne a ranar Litinin, 3 ga Afrilu, 2023 a Awon, karamar hukumar Kachia.

  • Da Dumi-Dumi: Fintiri Ya Kayar Da Binani A Kujerar Gwamnan Adamawa

Kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya ce bisa ga bayanan sirri da aka samu, daliban sun tsere ne daga wani dajin da ke kusa da kan iyakokin Kaduna da Neja.

Aruwan ya ce daliban sun yi tafiya na kwanaki kafin su isa wani wuri da ke da aminci wanda ba a bayyana sunan wurin ba sabida dalilan tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa daga bisani majiyoyin leken asiri sun sanar da gwamnatin jihar cewa, a yi gaggawar kwashe daliban daga garinsu.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Aruwan ya ci gaba da cewa Gwamna Nasir El-Rufai bayan samun bayanan sirrin, ya umurci ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida da ta tuntubi runduna ta 1 ta sojojin Nijeriya domin kwashe daliban cikin gaggawa zuwa babban birnin Kaduna, sabida an tattaro cewa ‘yan ta’addan sun kuduri aniyar sake sato daliban ta kowane irin hali.

Ya kara da cewa “An kwashe daliban zuwa wani wurin sojoji inda a yanzu haka suke samun kulawar likitoci.”

A halin da ake ciki, Gwamna El-Rufai ya bayyana jin dadinsa da samun wannan rahoto, kuma ya yabawa daliban bisa nuna jajircewa wajen ganin sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga G7 Ta Daina Bata Mata Suna Da Kuma Karkatar Da Hankalin Duniya

Next Post

An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

Related

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna
Labarai

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

2 hours ago
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

6 hours ago
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

8 hours ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

9 hours ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

9 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

10 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

An Kaddamar Da Bikin Haduwar Matasan Sin Da Afirka Karo Na 7

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.