• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Na Gaba Ake Gane Zurfin Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watan Satumba na shekarar 2020, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin na da burin kawar da sinadarin carbon dioxide kafin shekarar 2030, da kuma cimma matsaya game da kawar da iskar carbon gaba daya kafin shekarar 2060. A watan Nuwamban bana, a taron San Francisco, Sin da Amurka sun yanke shawarar yin hadin gwiwa a karkashin kungiyar aiki kan inganta yanayi. La’akari da ayyuka masu inganci wadanda ba a taba yin irinsu ba game da inganta yanayi, Sin ta zama babbar mai shiga tsakani, mai ba da gudummawa, kuma jagora a harkokin yanayi na duniya. Shi ya sa kasashen duniya suka sallama ma kasar Sin jagorancin magance sauyin yanayi saboda da na gaba ake gane zurfin ruwa.

Tarihi ya tabbatar da irin gwagwarmayar da kasar Sin ta yi kafin ta kai ga wannan matsayi na jagora a harkokin inganta yanayin duniya. A zamanin da, gidajen wanka na jama’a inda za ka biya kudi kadan sa’annan ka yi wanka da ruwan zafi sun kasance “ababen kallo” na musamman a biranen kasar Sin. Saboda ba a cikin sauki ake iya samun ruwan zafi na wanka a gidajen mutane ba.

  • An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023
  • Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu Sun Sake Karfafa Huldar Diflomasiyya

Amma a yau, wadannan gidajen wanka na jama’a wadanda ke fitar da iskar carbon mai dumama yanayi suna zama tarihi a hankali. Ci gaba a fannin fasahar samar da na’urar dafa ruwa mai amfani da hasken rana ta kawo sauki ga al’umma wajen samun biyan bukata ba tare da gurbata muhalli ba wanda ya daidaita kasar Sin a kan turbar rayuwa mai karancin iskar carbon.

Daga kayan masarufi masu aiki da makamashin hasken rana zuwa samar da wutar lantarki, kasar Sin ta kasance jagora a cikin masana’antar samar da makamashi bisa hasken rana. Sama da shekaru goma da suka gabata, masana’antar makamashin hasken rana ta kasar Sin ta dogara kacokan ga kasashen waje wajen samar da albarkatun kasa da fasaha.

A yau, kididdiga daga kungiyar masana’antun samar da makamashi bisa hasken rana ta kasar Sin ta nuna cewa kamfanonin kasar Sin suna matsayi na daya a harkar samar da abubuwa masu mahimmanci guda hudu wadanda ake sarrafa makamashin hasken rana da su wato polycrystalline silicon, silicon wafers, da baturun cell, da sauran jiga-jigan sarrafawa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Ci gaban da kasar Sin ta samu a masana’antar sarrafa wutar lantarki bisa hasken rana ya nuna aniyar kasar na aiwatar da manufofinta na fitar da karancin sinadarin carbon da kuma magance matsalar sauyin yanayi a duniya. Tun daga shekarar 2022, kasar Sin ta samu ci gaba cikin sauri a sabbin makamashi da suka hada da wutar lantarki mai aiki da hasken rana da kuma karfin iska, wanda ya haifar da raguwar dogaro da albarkatun waje na mai da iskar gas a cikin shekaru 30 da suka gabata.

A cewar hukumar kula da makamashi ta kasar, ya zuwa karshen watan Yunin shekarar 2023, karfin makamashin da ake sabuntawa da aka girka a kasar Sin ya zarce kilowatt biliyan 1.3, wanda a karon farko ya zarce karfin da aka girka na makamashin kwal a tarihin kasar Sin. Karfin wutar lantarkin kasar Sin bisa hasken rana da karfin iska, da ruwa, da nau’in makamashi daga wasu halittu yana kan gaba a duniya.
Kamar dai yadda wakilin shugaban kasar Sin Xi Jinping na musamman Ding Xuexiang ya bayyana a yayin taron koli kan harkokin yanayi na duniya da ya gudana a birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa, ya kamata dukkan bangarorin su karfafa azama wajen tinkarar kalubalen sauyin yanayi tare.

Yayin da take daukar kwararan matakai don yaki da dumamar yanayi, kasar Sin ta kuma bukaci kasashen duniya da su kiyaye manufofi da ka’idojin da aka gindaya a cikin yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD da yarjejeniyar Paris, da inganta hadin kai da hadin gwiwa, da samun moriyar juna da samun nasara tare. A yayin da ake fuskantar rikice-rikice a duniya, hadin gwiwa ce kawai mafita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSinTattalin arzikin kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Taron Fahimtar Sin Na shekarar 2023

Next Post

Harin Jirgin Sojin Nijeriya A Kan Taron Maulidi Ya Tayar Da Hankali A Kaduna

Related

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

13 hours ago
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
Daga Birnin Sin

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

13 hours ago
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

14 hours ago
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

14 hours ago
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

15 hours ago
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

15 hours ago
Next Post
Harin Jirgin Sojin Nijeriya A Kan Taron Maulidi Ya Tayar Da Hankali A Kaduna

Harin Jirgin Sojin Nijeriya A Kan Taron Maulidi Ya Tayar Da Hankali A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.