• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka ana gudanar da taron kasashen da suka sanya hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD ko COP27 a takaice, a wurin shakatawa na Sham El-Sheikh dake kasar Masar, inda shugabannin kasashen duniya za su tattauna kan matsalolin dake hana ruwa gudu game da magance matsalar sauyin yanayi dake ci gaba da addabar sassan duniya ta fannoni daban-daban.

Galibin shugabannin kasashen da suka gabatar da jawabai a taron na wannan karo, sun kara yin kira ne ga kasashe masu karfin tattalin arziki, da su dauki matakai na zahiri maimakon maganar fatar baki da suka saba yi a duk lokacin da aka kira irin wannan taro ko wani dandali mai kama da wannan, domin shawo kan illolin da sauyin yanayin ke haifarwa, kamar zafi da fari da ambaliyar ruwa da mahaukaciyar guguwa dake tafe da mamakon ruwan sama da makamantansu.

  • Masana Kimiya Na Kasashen Sin Da Kenya Sun Fara Girbin Nau’in Masara Mai Inganci

Haka kuma sun yi kashedin cewa, lokaci fa yana kurewa, kuma duk wani jan kafa kan wannan batu, babu abin zai haifar illa haddasa asarar rayuka da dukiyoyi. Yanzu haka ana kiyasin cewa, mutane miliyan 700, za su rasa muhallansu a nahiyar Afirka, sakamakon rashin ruwan sha nan da shekarar 2030.

Shi ma babban sakataren MDD Antonio Gutteres, ya shaidawa taron cewa, duniya ta doshi hanyar shiga bala’u na sauyin yanayi, wanda kusan kowa yana ganinsu a sassan duniya, kamar irin matsalolin da aka ambata a sama na ambaliyar ruwa da matsanancin fari da sauransu.

Wani rahoto da hukumar kula da makamashi ta MDD ya nuna cewa, a shekaru 8 dake tafe, ana iya cewa, duniya ta kama hanyar fuskantar zafi mafi tsanani a tarihi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Shin ina muka dosa? Hukumomin MDD gami da kungiyoyi masu zaman kansu ma, sun yi kashedin cewa, an samu karuwar matsalar karancin abinci mai gina jiki a cikin shirye-shiryen kula da abinci mai gina jiki a fadin yankin kahon Afirka, wannan ma wata alama ce ta matsalar sauyin yanayi, haka kuma mutane da dama sun rasa abubuwansu na rayuwa, da hanyoyin da za su iya magance wannan bala’i, sannan kuma sun dogara baki daya kan taimako don biyan bukatunsu na yau da kullum, matakin da zai iya kalubalantar farfadowar fari.

Yanzu dai dabara ta rage ga mai shiga rijiya. Ko dai duniya ta mayar da hankali wajen daukar managartan matakan magance wannan matsala ko kuma duniya ta ci gaba da shiga hali na garari sakamakon matsalar sauyin yanayi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fitar Da Takardar Bayani A Wajen Babban Taron Yanar Gizo Na Duniya Na Shekara Ta 2022

Next Post

Kwastam Sun Kama Kaya Da Motocin Alfarma Na Kimanin Miliyan 77 A Katsina

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

8 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

8 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

10 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

13 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

14 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
Kwastam Sun Kama Kaya Da Motocin Alfarma Na Kimanin Miliyan 77 A Katsina

Kwastam Sun Kama Kaya Da Motocin Alfarma Na Kimanin Miliyan 77 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.