• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daftarin Da Ya Shafi Jihar Xinjiang Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Daftarin Da Ya Shafi Jihar Xinjiang Na Da Nufin Dakile Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar kare hakkin bil Adama ta MDD, ta yi watsi da wani daftari da ya shafi jihar Xinjiang, wanda wakilin Sin ya bayyana a matsayin wani yunkuri na amfani da hukumomin kare hakkin dan Adam, domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Sin, da amfani da batutuwan da suka shafin Xinjiang domin dakile ci gaban kasar.

Chen Xu, shugaban tawagar kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva ne ya bayyana haka, inda ya ce Amurka da wasu kasashe ne suka shirya tare da gabatar da daftarin, suka kuma mika shi a matsayin matsalar dake bukatar gyara, a yunkurinsu na gaskata nazarinsu da ya sabawa doka, da sanya batutuwan da suka shafi Xinjiang da babu su a zahiri, a cikin ajandar majalisar.

  • Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Dakin Adana Kayan Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin Ta Samar

Ya bayyana gabanin kada kuri’a a jiya Alhamis, a zama na 51 na majalisar kare hakkin bil Adama cewa, batutuwan da suka shafi Xinjiang, ba su da alaka ko kadan da na hakkokin dan Adam, yana mai cewa, batutuwa ne da suka shafi yaki da ta’addanci da ra’ayi mai tsauri da kuma yaki da ‘yan aware.

Ya kuma shaidawa majalisar cewa, bisa namijin kokarin da aka yi, ba a samu ayyukan ta’addanci a Xinjiang ba, cikin shekaru 5 a jere. Kuma ana ba da cikakkiyar kariya ga hakkokin dukkan kabilun dake jihar.

A cewar Chen Xu, cikin sama da shekaru 60 da suka gabata, yawan al’ummar Uygur na Xinjiang ya karu daga miliyan 2.2, zuwa kusan miliyan 12, kuma matsakaicin shekarunsu na rayuwa ya karu daga 30 zuwa 74.7.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Ya ce ta hanyar yin biris da shaidu da gaskiya, Amurka da sauran wasu kasashe sun shirya tare da yada karairayi da jita-jita, a yunkurinsu na bata sunan Sin da kawo cikas ga zaman lafiya a jihar Xinjiang da dakile ci gaban kasar. Ya ce wannan misali ne na kulli irin na siyasa da take hakkin dan Adam mai tsanani, na dukkan kabilun jihar Xinjiang.

Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin ya bayyana a jiyan cewa, shaidu sun nuna sau da dama cewa, siyasantar da batun hakkin dan Adam, da nuna fuska biyu, ba za su yi tasiri ba, kuma yunkurin amfani da batutuwan da suka shafi jihar Xinjiang domin durkusarwa ko dakile kasar Sin ba zai yi nasara ba. (Fa’iza Msutapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Next Post

Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

40 minutes ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

2 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

3 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

4 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

23 hours ago
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

24 hours ago
Next Post
Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

Ya Yi Yunkurin Jefa Matarsa Rijiya Don Zargin Tana Cutarsa

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.