An yi nasarar gudanar da wani binciken aikin gona na hadin gwiwar Sin da Afirka wanda jami’ar koyon aikin gona ta kasar Sin ta shirya a birnin Wuwei na lardin Gansu dake arewa maso yammacin kasar Sin.
Aikin na mako guda mai suna China-Africa Oasis tare da yankin Gansu dake bakin kogin Shiyang, shi ne aikin farko na jami’ar da ya kunshi tawagar hadin gwiwa na daliban kasar Sin da kasashen Afirka, wadanda suka gudanar da ayyukan bincike mai inganci da suka mayar da hankali kan fasahar aikin gona da raya karkara.
Daliban kasar Sin goma da daliban Afirka 11 daga kasashe 10 ne suka halarci taron. (Mai fassara: Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp