• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Amai Da Gudawa Na Yara Lokacin Fitar Hakori

by Sulaiman and Bilkisu Tijjani
10 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Dalilan Amai Da Gudawa Na Yara Lokacin Fitar Hakori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Likitoci masana lafiyar kananan yara sun bayyana cewa, fitar da hakorin da yara suke yi ko kadan baya kawo gudawa ko amai kai-tsaye. Sai dai, mafi yawan al’umma na alakanta wasu abubuwa da ke faruwa lokacin fitar hakoran a matsayin musabbabin gudawa da aman da ke faruwa a daidai wannan lokaci. 

 

Wadannan abubuwa kuwa sun hada da:

1- Lokacin da yaro ke fara fitar da hakori, ya yi daidai da lokacin da ake fara bashi abincin gida (supplementary feeding), wanda rashin sabo da abincin kan iya bata masa ciki har ya sanya shi gudawa ko amai nan take. Cikin yaro kan dauki lokaci kafin ya saba da irin abincin da za a fara ba shi, musamman idan ya shafe wata shida ba ya shan komai sai mama.

2- Lokacin fara fitar hakori ya yi daidai da lokacin da yaro zai fara rasa sojojin garkuwar jikin da yake samu daga mahaifiyarsa a lokacin da ta haife shi. Rasa Wadannan sojojin garkuwar jiki, kan raunana garkuwar jikinsa na dan wani lokaci kafin tasa garkuwar jikin ta yi karfi. Wannan raunin kan sa ‘yan cututtuka kadan su sanya yaro gudawa, amai, zazzabi ko kuma zafin jiki.

Labarai Masu Nasaba

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Watakila mai karatu zai yi mamaki, idan aka ce garkuwar jikin jariri sabon haihuwa ta fi ta dan wata shida karfi, wannan ba abin mamaki ba ne; saboda idan aka haifi yaro akwai sashen wasu sojojin garkuwar jikin mahaifiyasa da za su biyo shi su taimaka masa, domin fada da cututtuka. Wadannan sojojin ba sa iya wuce wata shida suna aiki a jikin yaro, daga nan kuma za su mutu su bar yaro da garkuwar jikinsa matashiya.

3- A lokacin fitar da hakora, dasashin yaro ya kan dan yi kumburi ya fara kaikayi da ciwo a wajen da hakoran za su fito, wannan shi zai sa yaro ya kama sanya hannu a baki da kuma duk abin da ya samu; sai ya sa a cikin bakin nasa, domin ya ji saukin wannan kaikayi da ciwo da suke damun sa. Sanya abubuwa da dama wadanda ba a tsafta ce ba a cikin baki, kan sanya yaro kamuwa da kananan cututtukan da za su haifar masa da amai da kuma gudawa. Bugu da kari, garkuwar jikin yaro a wannan lokaci na fuskantar barazana; kamar yadda muka yi bayani a baya, saboda haka; ba za ta iya yin fada da kananan cututtukan ba.

4- A lokacin fitar da hakora, a kan samu karin fitar da yawu da kuma wasu sinadaran ‘cytokines’ daga cikin jikin yaro. Wannan shi kadai ya kan iya yin sanadiyyar tsinkewar bahayar yaro.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin SADC Za Su Hallara A Sabon Ginin Ofishin Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa Domin Gudanar Da Taron Shekara

Next Post

Jirgin Ruwan Sin Mai Dauke Da Asibitin Tafi Da Gidanka Ya Kammala Aiki A Mozambique

Related

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

6 days ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

7 days ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

3 weeks ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

1 month ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

2 months ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Next Post
Jirgin Ruwan Sin Mai Dauke Da Asibitin Tafi Da Gidanka Ya Kammala Aiki A Mozambique

Jirgin Ruwan Sin Mai Dauke Da Asibitin Tafi Da Gidanka Ya Kammala Aiki A Mozambique

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.