Dan wasan Damben Boxing dan asalin Nijeriya, Anthony Joshua, ya saka karfin damtse wajen doke abokin karawarsa, Francis Ngannou, a zagaye na biyu na wasan damben da suka buga a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.
Joshua mai shekaru 34 ya baje zakaran gasar damben UFC a kasa har sau biyu a zagayen farko da na biyu na wasan wanda ya ja hankalin masu sha’awar kallon damben turawa.
- An Kammala Wasan Karshen Damben Warriors Na Wannan Shekarar A Kano
- Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola
Da wannan nasarar ta Joshua ita ce ta 4 cikin nasarorin da ya samu cikin watanni 11, yayin da yake neman dawo da kambunsa na gwarzon Duniya a fagen damben Boxing wanda ya taba rikawa a baya.
Joshua da Ngannou dukkansu bakaken fata ne, inda Anthony Joshua yake da tsatso a Nijeriya, shi kuma Francis Ngannou dan asalin kasar Kamaru ne kuma dukkansu sun lashe manyan kambunan wasan dambe kafin su hadu da junansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp