• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan Jihar Ogun Na PRP Bamgbose Ya Mutu , Yana Da Shekara 54

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Ogun

Kasa da ‘yan makwanni kalilan da samun nasarar tikitin takara na jam’iyyar sa, dan takarar gwamnan Jihar Ogun a karkashin lemar Peoples Redemption Party (PRP), Farfesa David Olufemi Bamgbose, ya mutu.

Dattijon mai shekara 54 a duniya ya kasance mai taimakon al’umma kuma Farfesa ne a sashin ilimi (education) ya mutu ne a ranar Juma’a a asibitin Sacred Heart da ke Lantoro, Abeokuta, inda aka kwantar da shi domin jinyar gajeruwar rashin lafiya da ta sameshi.

  • Zulum Ya Shigar Da Marayu 7000 Makaranta A Monguno
  • Yadda Rugujewar Gadar Katarko Ta Katse Yobe Da Jihohin Borno Da Gombe

LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Alhamis ne marigayi Bamgbose ya yi korafin rashin lafiya inda makusantansa suka garzaya da shi wani asibiti mai zaman kansa da ke rukunin gidajen ‘yan gaju (FHE) da ke Olomoore a yankin Abeokuta yayin da kuma aka canza masa asibiti zuwa babban asibitin Gwamnatin tarayya (FMC) da me Abeokuta.

Hadimin mamacin, Oduntan Olayemi, shine ya tabbatar da mutuwar mai gidan nasa a lokacin da ke zantawa da ‘yan jarida a Abeokuta, ya yi bayanin cewa an sanya marigayin a na’urar da ke taimakawa numfashi a asibitin Sacred Heart har zuwa ranar Juma’ar lokacin da rai ya yi halinsa.

Ya ce kafin ya mutu ya yi ta harba numfashi sosai inda aka yi kokarin kula da shi amma kwana ya kare.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Bamgbose dai ya fice daga jam’iyyar PDP inda ya shiga cikin PRP a kwanakin baya.

Kafin nan a zaben 2015 ne ya kasance dan takarar gwamna na jihar Ogun a karkashin jam’iyyar APGA.

Ya kasance wanda ya lashe zaben fitar da gwani na jam’iyyar PRP na zaben 2023 da ke tafe wanda aka gudanar a ofishin NUJ da ke Iwe Irohin, Abeokuta, babban birnin jihar.

Marigayin Farfesa ne a jami’ar European America University, kafin mutuwarsa babban Minista ne a cocin Peace and Love Church of God, da ke yankin Ogbe a cikin Abeokuta, ya mutu ya bar matarsa Misis Mary Bamgbose da yara shida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Majalisar Dattawa Na Neman A Kara Harajin Ilimin Manyan Makarantu

Majalisar Dattawa Na Neman A Kara Harajin Ilimin Manyan Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.