• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

by Sulaiman
3 months ago
Dangote

Kamfanin Siminti na Dangote ya bukaci masu ruwa da tsaki a harkar samar da gidaje da su yi la’akari da tsarin samar da gidaje ga ‘yan Nijeriya da ya dace da daidai kasafin kudin masu karamin karfi.

 

Da yake jawabi a wajen bikin baje kolin gidaje na kasa da kasa na Afirka, Daraktan tallace-tallace na Kamfanin Siminti na Dangote, Dolapo Alli, ya ce: “Maganin matsalolin gidaje na bukatar hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki, da suka hada da hukumomin gwamnati, masu zaman kansu, da al’ummomi. Gwamnati za ta iya rungumar tsarin hadin gwiwa da kamfanoni masu zaman kansu don samar da gidaje masu rahusa ga al’umma wanda aka fi sani da shirin PPP.

  • Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
  • Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

“Ta hanyar tsarin PPP, gwamnati na iya ƙaddamar da gina sabbin gidaje, yayin da kamfanoni masu zaman kansu dake masana’antar gine-gine kuma a saukake musu haraji tare da basu lamuni don saukake samar da kudade na sababbin gidaje masu rahusa.”

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Mista Alli, wanda yake jawabi a rana ta musamman ta kamfanin, ya ce, samar da gidaje masu yawa na daya daga cikin dabaru da dama da ake amfani da su wajen magance kalubalen karancin gidaje ga jama’a, inda ya kara da cewa, amma wannan tsarin ya taimaka wajen magance matsalolin da ke tattare da saurin bunkasar birane a kasashe da dama na duniya.

 

Ya yabawa kokarin Gwamnatin Tarayya wajen aiwatar da shirye-shiryen samar da gidaje masu yawa, inda ya kara da cewa, amma akwai bukatar a cike gibi.

 

Ya ce: “Nijeriya, ta hanyar shirin sabunta fata na samar da gidaje da gwamnatin shugaba Tinubu ta kirkiro, ta dauki matakan yabawa wajen magance babban gibin da ke tattare da samun lamunin kudade wajen samar da gidaje masu rahusa. Wannan shiri na nuni da cewa, an himmatu wajen ganin ‘yan kasa sun samu saukin mallakar gidaje, musamman masu karamin karfi da matsakaita tattalin arziki.

 

Ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su aiwatar da ingantattun tsare-tsare tare da samar da filayen gina gidaje masu tarin yawa a Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti na Dangote na daya daga cikin masu daukar nauyin shirin baje kolin gidaje na Afirka (AIHS) wanda za a rufe ranar Juma’a 1 ga Agusta, 2025.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Next Post
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

LABARAI MASU NASABA

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.