• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF

byYusuf Shuaibu
10 months ago
Arewa

Wasu jiga-jigan masu fada a ji a yankin arewa sun shiga tsakani don warware rikicin siyasar da kunno kai bayan dakatarwar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar Arewa ‘Consultatibe Forum’ (ACF), Mista Mamman Mike Osuman.

Mataimakin Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT), Ambasada Ibrahim Maisule ne ya tabbatar da hakan a wata tattaunawa ta musamman a Abuja.

  •  Ali Nuhu Ya Zama Jakadan Kamfanin Tsaftace Haƙora A Arewacin Nijeriya 
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

A karshen makon da ya gabata ne dai aka dakatar da shugaban kwamitin zartarwa na kungiyar ACF bisa wasu kalamai da ya yi da suka shafi siyasa, wadanda kwamitin amintattu da wasu mambobin kungiyar suka yi watsi da su.

A cikin wata wasika tare da sa hannun babban sakataren kungiyar ACF, Malam Murtala Aliyu da shugabannin BoT, Alhaji Bashir Dalhatu, Mista Osuman, an zargi Mista Osuman da yin kalamai marasa izini da ke nuna cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027.

Wasikar ta ci gaba da cewa, “An jawo hankalin kungiyar kan wasu bayanai da aka rika yadawa ga Mista Mamman Mike Osuman, SAN, OFR, Shugaban kwamitin zartarwa na ACF na kasa, wadanda aka yi a yayin taron kungiyar wanda aka yi a ranar Laraba, 20 ga Nuwamba, 2024, a hedkwatar ACF da ke Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“An ji Mista Osuman yana cewa arewa za ta mara wa dan takarar shugaban kasa daga arewa baya a 2027. Shugaban kungiyar ya yi wadannan kalamai ne ba tare da tuntuba ko tattaunawa da wasu shugabanni da mambobin kungiyar ta ACF ba, don haka ya nuna ra’ayinsa ne kwai.

“ACF ta yi watsi da kalaman Mista Mamman Mike Osuman gaba daya. Don haka ne shugabannin kwamitin amintattu na ACF (BOT) da na gudanarwa ta NEC suka yanke shawarar dakatar da Mista Mamman Mike Osuman nan take.”

Sai dai Mista Osuman, ya yi zargin cewa ba a yi masa adalci ba wajen tsarin da aka bi na dakatar da shi.

An dai bayyana cewa, Mista Osuman ya tara tawagar manyan lauyoyin ne tun a karshen makon da ya gabata, a shirye-shiryen shigar da karar na kalubalantar dakatar da shi daga mukaminsa.

Wasu majiyoyi na kusa da shi sun ce ya tattara manyan lauyoyin Nijeriya guda takwas masu mukamin SANs da nufin kalubalantar dakatar da shi a kotu.

Bugu da kari, wasu majiyoyi na kusa da BoT da kuma NEC na kungiyar sun shaida cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Alhaji Mahmud Yayale Ahmed ya kira taron masu ruwa da tsaki a ranar Talata a Abuja, inda suka tattauna kan bukatar gaggawa don magance rikicin wajen guje jefa ACF cikin wani babban rikicin siyasa.

An tattaro cewa, za a ci gaba da taron ne a ranar Asabar, yayin da karin shugabanni a yankin arewa ke kokarin ganin an shawo kan rikicin cikin gaggawa.

Ambasada Maisule ya bayyana kwarin gwiwa game da shirin sulhun, inda ya ce dattawan yankin sun dukufa wajen ganin an warware matsalar.

“Mutane suna yin kuskure a kowani lokaci, mu mutane ne amma kuskure ba za a taba sanya shi ba a matsayin daidai. Don haka dole ne a nemo mafita.

“Tattaunawa da cikakkun bayanai a bainar jama’a yanzu bai zama dole ba, saboda an riga an yi wani babban yunkuri na warware rikicin. Wadanda ke da hannu a cikin yunkurin suna da himma sosai kuma suna iya aikin.

“Na yi imani da iyawarsu na nemo hanyar warware matsalar, kuma ina da kyakkyawan fata game da sakamakon lamarin. A wurina, babban abu mai muhimmanci shi ne, kawar zargi tare da tallafa wa tsarin don tabbatar da ci gaba. A nan ne hankalina ya karkata,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version