• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

by Sani Anwar and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 12 ga watan Yuni ranar tunawa da mulkin Dimokuradiyya muhimmiyar rana ce a farfajiyar siyasa da mulki a Nijeriya wadda kima da tasirin ta ya fi gaban a nanata.

‘Yan Nijeriya na tunawa da ranar ce da aka gudanar da zaben Nijeriya na 1993, duk da yake hukumar zabe ba ta bayyana sakamakon zaben ba saboda soke shi da gwamnatin Babangida ta yi, sai dai alamomi sun nuna Moshood Abiola na jam’iyyar SDP ne ya yi galaba kan Bashir Tofa na NRC.

Daga 1999 lokacin da sojoji suka koma bariki a yayin da Janar Abdulsalam Abubakar ya hannun ta mulki a hannun gwamnatin farar hula ta farko a karkashin jagorancin shugaba Obasanjo, ranar 29 ga Mayu ce ranar dimokuradiyya wadda shugaba Muhammadu Buhari ya canza zuwa 12 ga Yuni a shekarar 2018.

A yau da Nijeriya ke bukin cika shekaru 26 cur a saman tafarkin mulkin dimokuradiyya ba tare da kowace irin tangarda daga sojoji ba, daga wannan gwamnatin zuwa waccan a bayyane za a ce an samu ci-gaba sosai da kuma ci-baya a tsakanin wadannan shekarun a kowane irin fanni na mulki da siyasa.

‘Yan kasa da dama na bayyana ci-gaban da aka samu a tsayin wadannan shekarun a matsayin ci-gaban mai hakar rijiya kansancewar har yau kasar ba ta tsayu da kafafun ta ba ballantana ta kai matakin da ya kamata ta kai musamman yadda wasu kasashen Afrika da dama suka shiga gaban ta.

Labarai Masu Nasaba

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

A tsayin wadannan shekarun, Nijeriya ta fuskanci kalubale da dama da suka hada da fafutukar tabbatar da mulkin dimokuradiyya, siyasar yanki, rikita- rikitar addini da kabilanci da kuma gagarumar matsalar tsaro daga Kudu zuwa Arewa.

Mafi yawan al’ummar Nijeriya na bayyana shekaru 26 na mulkin dimokuradiyya a matsayin shekarun gurbataccen mulki, shekarun mulkin danniya da zalunci, cin hanci da rashawa, tabarbarewar tsaro, rugujewar tattalin arziki kana shekaru 26 na satar danyen mai, rashin wutar lantarki, koma baya a sha’anin ilimi, aikin gona da rashin ayyukan yi tare da hauhawar farashin mai da tsadar rayuwa.

Akasin murnar wannan ranar, kungiyoyi a Arewa da Kudu, jam’iyyun siyasa, kungiyoyin farar hula da na matasa da dalibai sun bayyana ‘yan siyasa a matsayin matsalar da ta dabaibaye kasar nan ba wai tsarin aikin gwamnati ba.

A mabambantan bayan su kungiyar dattawan Arewa ta ACF, kungiyar Yarbawa ta Afenifere da Ohanaeze ta Inyamurai sun bayyana amfani, nasarori, illa da matsalolin mulkin dimokuradiyya.

Kungiyar dattawan Arewa ta ce matukar ‘yan siyasa ba su watsar da tsattsauran ra’ayin su na rikau, talakawa ba za su mori romon mulkin dimokuradiyya ba. Ita kuwa kungiyar Yarbawa ta bayyana kima da tasirin mulkin dimokuradiyya ga kasa da ‘yan kasa, sai dai duk da kasawarsa a wasu bangarori ta ce shine tsari mafi inganci ga ‘yan Nijeriya.

Sai dai kungiyar Inyamurai ta bayyana cewar babu wata mafita ta samar da ci-gaba a Nijeriya illa canza fasalin kasa domin a baiwa kowane yanki damar bunkasa tattalin arzikin sa.

Haka ma kungiyoyi da dama sun koka ga gwamnati a kan ta gaggauta shawo kan matsalolin tsadar rayuwa, rage farashin mai da bunkasa tattalin arziki wadanda suka zama silar jefa al’umma a cikin kunci musamman a dalilin cire tallafin man fetur da wasu tsare-tsaren gwamnati masu tsauri.

A cewarsu maimakon shagalin buki, kamata ya yi a yi zaman jajantawa juna kan gurbatacciyar hanyar da shugabannin kasar mabambanta suka hau na rashin ci-gaba akasin ingantacciyar hanyar da shugabannin baya wadanda suka jagoranci samarwa kasar ‘yanci suka dora ta a kai.

Da yawan mutane sun yi tunanin daga shekarar 1999 zuwa yau matsalolin da ake fuskanta za su kau amma sai a ka ga akasin hakan. Abubuwan da ke ciwa jama’a tuwo a kwarya musamman sha’anin samar da hasken wutar lantarki har yanzu ba a shawo kan matsalar ba duk da irin makuddan kudaden da a ka narkar wadanda a ke ganin bai kamata a ce har yanzu babu tsayayyiyar wutar lantarki a Nijeriya.

A ra’ayin wasu gwamnatoci a mataki-mataki sun taka rawar gani. Idan da a ce babu mulkin dimokuradiyya da ba za a samu ‘yancin fadar albarkacin baki ba wanda shi kansa ci-gaba ne.

Haka ma a cewar su idan aka kalli kauyukan kasar nan a kananan hukumomi 774 zuwa yau an samu ci-gaba domin a can baya ba haka suke ba. Sai dai tabbas ci-gaban ba yadda a ka zata ba ne. Watakila gwamnatocin ba su samu kudade yadda ya kamata ba, wasu kuma na kukan matsalar daga hannun shugabanni take.

Mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a tsayin wadannan shekaru mulki ne da ke cike da rudu da kwamacalar siyasa daban-daban. A wanann rahoton za mu gabatar da muhimman abubuwan da dama da suka faru a kowace gwamnatin dimokuradiyya daga Obasanjo, ‘Yar’Adua, Jonathan, Buhari zuwa Tinubu da ke jan zaren mulki a yau.

 

Abubuwan Tunawa A Gwamnatin Obasanjo (1999-2007)

A jiya da yau a kan tuna da Gwamnatin Obasanjo a 1999-2007 ta hanyar kafa Hukumomin Yaki da Almundana da Kudaden Al’umma (EFCC) da (ICPC) tare da karfafawa Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata domin yaki da cin hanci da rashawa. Gurbatattun ‘yan siyasa da mutane da dama sun shiga hannu tare da gurfana a kotu zuwa daurewa a kurkuku a wancan lokacin.

Wasu daga cikin nasarorin da za a iya cewa gwamnatin Obasanjo ta samarwa al’ummarta akwai rattaba hannun shigowa da kamfunan sadarwa wanda ya zama silar samar da wayoyin hannu na GSM wanda daga lokacin zuwa yau kusan babu wani gida a Nijeriya da ba a mallakin wayar tafi-da-gidanka ba.

Gwamnatin Obasanjo wadda aka samu tabarbarewar tsaro da rikita- riikitar kabilanci a mulkinsa haka ma a mulkin sa an shaidi yawaitar faduwar jiragen sama ciki har da jirgin ADC wanda ya dauki rayuwar Sarkin Musulmi Muhammadu Maccido da muhimman mutane a 2006.

Gwamnatin Obasanjo ta yi matukar kokarin samarwa Nijeriya afuwar bashin zunzurutun kudi har dala Biliyan 18 daga Paris da London wanda ya jima yana ciwa kasar nan tuwo a kwarya.

Bugu da kari a zamanin mulkin Obasanjo ne siyasar ko- a- mutu- ko- a- yi-rai ta samu gindin zama ta yadda aka rika sarawa ko babu gaba ga duk wani ko wadanda suka yi kokarin shiga gona ko huruminsa. Obasanjo a 2007 a kokarin sharewa marigayi ‘Yar’Adua hanyar zama shugaban kasa, ya jagoranci gudanar da kazamin zabe mafi muni a Nijeriya wanda ke cike da aika-aika da murdiyar zabe.

Haka ma Obasanjo ya so yi wa mulkin dimokuradiyya fyade a yayin neman zarcewa saman mulki a wa’adi na uku lamarin da ‘yan Nijeriya suka sa kafa suka shure tare da Allah-wadai kan kokarin yin karan tsaye ga kundin tsarin mulkin kasa, abin da ya kawo karshen bukatarsa wadda hakarsa ta kasa cimma ruwa.

 

Umaru ‘Yar’Adua (2007-2010)

Umaru Musa ‘Yar’Adua shine shugaban Nijeriya daga Mayu 2007 zuwa 5 ga Mayu 2010 a lokacin da ya yi bankwana da duniya yana a saman mulki.

‘Yar’Adua ne shugaban kasa na farko a tarihi da ya fara bayyana kadarorin da ya mallaka a bayyane tun kafin ya shiga ofis. Haka ma a fili ya fito ya bayyanawa duniya cewar zaben da ya kawo shi saman mulki cike yake da ta’addanci, murdiya da sabawa dokokin zabe.

Haka ma gwamnatin Matawallen na Katsina ta taka rawar gani wajen rage farashin man fetur daga farashin da yake akai zuwa naira 65 a kowace lita. Dukkanin gwamnatocin baya kara farashin mai suke yi, ita kuwa ta ‘Yar’Adua saukar da farashin ta yi. Kazalika takaitacciyar gwamnatin ‘Yar’Adua wadda ba ta yi tsawon rai ba ta cancanci a yaba mata wajen kawo gyara ga dokokin zabe.

Baya ga wannan a mulkinsa ba za a manta da yadda ya sa kafa ya sabawa tsarin mulki wajen rashin hannuntawa mataimakinsa Jonathan ragamar mulki ba a yayin da ya bar kasa zuwa duba lafiyarsa a Saudi Arabiya. Sai dai ‘yan Nijeriya masu kishi da hangen nesa sun tashi tsaye suka jagoranci gyara babbar matsalar tare da tabbatar da zaman Jonathan a matsayin mukaddashin shugaban kasa.

Haka ma gwamnatin ‘Yar’Adua ta samu nasarar kawo karshen ta’addancin tsagerun yankin Neja-Delta da ke talauta kasa ta hanyar yi masu afuwa suka ajiye mukamai tare da tallafa masu a shirin musamman wanda a lokacin ya kawo karshen ta’addanci a yankin mai albarkar man fetur.

 

Goodluck Jonathan (2010-2015)

A zamanin gwamnatin Jonathan ‘yan ta’addan Boko-Haram sun ci karensu ba babbaka ta yadda al’ummar kasa suka rika bacci da ido daya a gwamnatin Jonathan wanda shine shugaban kasa na farko da ya fito daga yankin Kudu-Maso-Kudu.

Sace ‘yan matan Chibok 100 da mayakan Boko-Haram suka yi awon gaba da su a makarantar mata a Jihar Borno a Afrilu 2014 lamari ne da ya yi matukar jan hankalin al’ummar ciki da wajen kasar nan.

Jonathan ya zama shugaban kasa na farko a tarihi kasar nan da ya sha kasa a zabe yana kan gadon mulki. Fitowa fili da ya yi ya karbi faduwa zabe tare da taya Muhammadu Buhari murna ya daga darajarsa da samar masa kima da dattako tare da tabbatar da karfin mulkin dimokuradiyya.

 

Muhammadu Buhari (2015- 2023)

Muhammadu Buhari wanda ya zama shugaban kasa a 2015 bayan ya sha kaye a zabukan 2003, 2007 da 2011, ya sake lashe zaben 2019 da gagarumar nasara.

Gwamnatin Buhari wadda ta yi kaurin suna wajen yekuwar yaki da cin hanci da rashawa, ta fadi kasa warwas ta hanyar kasa magance yawaitar cin hanci a fannoni da dama lamarin da jama’a ke ganin batun yaki da cin hanci suna ne kawai a gwamnatin Buhari domin kuwa a yayin da ake gurfanar da magoya bayan PDP a kotu, takwarorinsu na APC suna ci-gaba da cin karensu ba babbbaka a matsayin shafaffu da mai.

Bugu da kari gwamnatin Buhari ta kasance ta farko a dimokuradiyyar kasar nan da ta rika kawar da kai ga mutunta kundin tsarin mulkin kasa ta hanyar katsalandan ga sashen shari’a da rashin mutunta umurnin kotuna.

Misali kotuna daya bayan daya har guda tara sun bayar da belin Sambo Dasuki rsohon mashawarci na musamman kan sha’anin tsaro a gwamnatin Jonathan amma kuma gwamnatin Buhari ta kasa sakinsa a daurin da ta yi masa a kusan shekaru hudu kan badakalar kudin makamai.

A karkashin mulkin dimokuradiyya a zamanin Buhari al’ummar Nijeriya sun fuskanci yawaitar kisan gilla, garkuwa da mutane da ta’addancin Fulani fiye da kowane lokaci gabaninsa wanda bakidaya al’umma musamman a yankin Arewa suke cikin zullumi da fargaba. Haka ma Buhari zai ci-gaba da zama a cikin tarihi a matsayin shugaban kasa da ya kwashe kwanaki 217 wajen duba lafiyarsa a wajen kasar nan.

 

Bola Tinubu 2023-

A shekaru biyu na mulkin Bola Ahmad Tinubu al’ummar kasa na kuka da kokawa da tsare- tsare da manufofin gwamnatinsa masu tsauri ta yadda da yawa ke kewa da kwadayin mulkin PDP wanda rayuwa ke da sauki a mulkin ta.

Cire tallafin man fetur da Tinubu ya yi a jawabinsa na karbar mulki a 2023 shine babban abin da ya dauki hankalin jama’a tare da girgiza su musamman bisa ga radadi da kuncin da matakin ya jefa kasa da ‘yan kasa a ciki wanda ya haddasa tsada da karancin man fetur a lokaci daya.

Ya zuwa yanzu al’umma na cike da kunci a dalilin hauhawar farashin dukkanin abubuwan da rai ke bukata ta yadda abubuwa da dama musamman abinci ke gagarar talaka.

Duk da cewar farashin abinci yana tashi sama a fadin kasa a tsayin shekaru, amma yanayin a wannan lokacin ya ta’azzara ne sosai a bisa ga illar shiraruwan gwamnati musamman cire tallafin man fetur, faduwar darajar naira da sauransu.

 

Karuwar Talauci

Al’ummar Nijeriya da ke fama da talauci a zamanin gwamnafin da ta gabata sun kara talaucewa sosai a cikin shekaru biyu na mulkin Tinubu ta yadda a yau suke zumudin zuwan lokacin zabe.

Tsananin talaucin da al’umma ke fama da shi a yanzu, ya sa mafi yawan jama’a kasancewa cikin kuka da kokawa da yadda mulkin Tinubu ya zo masu wanda a baya suke fatar samun saukin al’amurra bayan karewar gwamnatin da ta gabata, amma sai gashi talaucin da ake fama da shi a yanzu ya fi na baya tsanani.

 

Matsalolin Tsaro

Duk da matakan da gwamnati ke dauka na kokarin samar da ingantaccen tsaro har zuwa yanzu ‘yan ta’adda na ci-gaba da cin karensu ba babbaka ta yadda suke hanawa al’umma bacci da idanu biyu wanda kasawa ce karara ga gwamnati a shekaru 26 na mulkin dimokuradiyya amma a kullum tsaron kasa kara tabarbarewa yake yi.

A yayin jin ra’ayin mabanbantan al’ummar kasa daga Arewa har Kudu kan amfani da alfanun da suka amfana da shi na romon mulkin dimokuradiyya, da yawa daga ciki sun bayyana shekaru 26 na dimokuradiyya a Nijeriya a matsayin shekarun gurbatacciyar dimokuradiyya, mulkin fatara da talauci, mulkin rikice-rikice da tashe-tashen hankula.

Bugu da kari jama’a sun fassara 26 a matsayin shekarun cin hanci da rashawa, shekarun sata da wawashe kudaden al’umma, kazalika shekarun karawa masu karfi karfi da kuma ci- da gumin talaka.

A kan wannan karara a yayin da wasu ke bayyana mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a matsayin wata hular baka ce wasu kuwa cewa suke yi Shekaru 26 Na Mulkin Dimokuradiyya A Nijeriya: Da Dadi, Ba Badi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Next Post

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Related

Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

8 minutes ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

1 hour ago
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

9 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

13 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

15 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

15 hours ago
Next Post
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

July 5, 2025
Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

July 5, 2025
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

July 5, 2025
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.