• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Tsakuwa

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya sanya hannu kan dokar majalisar gudanarwar kasar Sin, mai kunshe da matakan dakile takunkuman kasashen waje ta jamhuriyar jama’ar kasar Sin, a jiya Litinin.

Zan iya cewa, wannan doka ta zo a dai-dai lokacin da ake matukar bukatarta, bisa la’akari da yadda wasu ’yan tsirarrun kasashe ke kakaba takunkumai bisa radin kansu domin cimma wani buri na kashin kai. Kana akasarin irin wadannan takunkumai kan haifar da illa maimakon gyara duba da cewa dama an yi su ne bisa son kai. Takunkumai irin wadanda bangare guda ke dauka, kan kawo tsaiko ga harkokin da suka shafi cinikayya da dangantaka tsakanin kasa da kasa, har ma da zaman lafiyar duniya da hadin gwiwar kasa da kasa.

  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025

Tarihi ya nuna cewa, ba a taba amfani da tukunkumai akai-akai kamar a yanzu ba, haka kuma yawan wadanda ake kakabawa takunkuman, ya fi yawa a yanzu. Tabbas kakaba takunkumi kan yi amfani idan aka yi bisa ka’ida da zurfin tunani da kyakkyawar niyyar gyara, kuma bisa rinjayen kasashe maimakon kasa daya tilo ko ’yan tsiraru.

Sai dai a yanzu kasashe musamman Amurka, kan kakaba takunkumai ne domin cimma wani buri da tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe. Mun ga yadda ta rika kakaba takunkumai kan batutuwan da suka shafi jihar Xinjiang da Hong Kong bisa fakewa da batun kare hakkin bil adama. Sai dai, takunkuman nata, illa suke neman haifarwa da dakile ci gaban kasar Sin da zaman lafiyar da al’ummar kasar ke mora.

Kowace ’yantacciyar kasa na da ikon tsarawa ko zabar manufofi da hanyoyin da suka dace da yanayinta da al’ummarta, kuma duk mun san cewa, moriyar al’umma shi ne gaba da komai cikin manufofi da ayyukan gwamnatin kasar Sin. Don haka, lokaci ya yi da ya kamata Sin ta tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro, ta dauki matakan martani bisa dokokin kasa da kasa, domin jan kunne ga kasashen dake takalarta da neman ganin faduwarta. (Fa’iza Muhammad Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya
Daga Birnin Sin

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Next Post
Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa

Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.