• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubun Wata Budurwa Da Wasu 5 Ya Cika Bayan Ta Sace Wayoyin Salula 30 Na Matan Aure A Kano

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Dubun Wata Budurwa Da Wasu 5 Ya Cika Bayan Ta Sace Wayoyin Salula 30 Na Matan Aure A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta cafke wata budurwa da ta kware wajen satar wayar matan Aure bayan sun bata aminci a jihar.

 

Budurwar mai suna Shamsiyya Adamu ‘yar shekara 19, ta shiga hannu ne tare da abokan aikinta su biyar, an gano ta ne biyo bayan korafe-korafen jama’a da aka shafe watanni ana yi kan yawaitar satar wayar salula a cikin birnin Kano.

  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano
  • Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Yarinya Ɗaya da Mutum 2 A Kaduna

A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, Shamsiyya, wacce ke zaune a Birget kwatas a Kano, ta dauki hayar dan Adaidai da wanda ya kware wajen fasa asusun banki ta wayar salula, in ta afka gidan matan Aure sai ta yaudare su ta sace wayar, dan Adaidaita kuma yana jira a waje, sai ya kai ta wurin mai fasa asusun banki, ya kwashe kudaden wacce aka sace ma wayar.

 

Labarai Masu Nasaba

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Kamen da aka yi mata a ranar 21 ga watan Disamba, 2024, ya kawo karshen binciken da wata runduna ta musamman da kwamishinan ‘yansanda, CP Salman Dogo Garba ya kaddamar kuma ya jagoranta.

 

Wadanda aka kama dake aiki da ita akwai Idris Yusuf, dan shekara 23, mai sana’ar Adaidaita da ke tuka Shamsiyya zuwa wuraren da take aikata laifuka; Al’asan Dahiru, mai shekaru 24, wanda ya kware wajen boye kayayyakin da aka sace; Abdulmajid Haruna, mai shekaru 27, mai siyan kayan sata, wanda aka kwato wayoyi shida daga hannunsa, da Salim Auwalu, mai shekaru 21, wanda ya kware wajen fitar da kudi daga asusun ajiyar banki.

 

Rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa an shigar da kararraki 30 a kan Shamsiyya kan satar waya ta hanyar yaudara, 29 daga cikinsu mata ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Kudin Da Sin Ta Zuba Kan Layin Dogo Ya Kai Dala Biliyan 117 a 2024

Next Post

Ballon D’or: An Zaɓe Ni Ne Kamar Yadda Aka Zaɓe Ka – Martanin Rodri Ga Ronaldo

Related

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

6 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

7 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Manyan Labarai

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

8 hours ago
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3
Manyan Labarai

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

10 hours ago
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Manyan Labarai

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

15 hours ago
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

1 day ago
Next Post
Ballon D’or: An Zaɓe Ni Ne Kamar Yadda Aka Zaɓe Ka – Martanin Rodri Ga Ronaldo

Ballon D'or: An Zaɓe Ni Ne Kamar Yadda Aka Zaɓe Ka - Martanin Rodri Ga Ronaldo

LABARAI MASU NASABA

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.