• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Za Ta Dandana Kudar Matakin Da Amurka Ta Dauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ran 3 ga watan nan, babban bankin Amurka ya sake sanar da kara kudin ruwa da kashi 0.75%, da nufin sassauta hauhawar farashin kayayyaki a cikin gida. Yau “duniya a zanen MINA” zai bayyana muku illar da wannan mataki zai haifar.

Wannan shi ne karo na 6 da babban bankin Amurka ya kara kudin ruwa tun farkon bana, matakin da ya sa kudin ruwan ya kai matsayin koli tun watan Jarairu na shekarar 2008.

  • Tsegunta Barazanar Tsaro Daga Ofishin Jakadancin Amurka: Wa Abin Zai Amfanar?

Sai dai ba a kai ga daidaita matsalar hauhawar farashin kaya ba, a maimakon haka, matakin ya kara haifar da koma bayan tattalin arzikin duniya.

Bankin duniya ya ba da rahoto cewa, yawancin manyan bankunan kasa da kasa sun kara kudin ruwa a kasashensu da ba a taba ganin irinsa ba a cikin shekaru 50 da suka gabata sakamakon matakin da Amurka ta dauka. Abin da ya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa wadanda ke matukar bukatar ci gaba.

Kwanan baya, an saurari ra’ayin masana tattalin arziki 100 a duniya, inda suke ganin cewa, kudin ruwan da Amurka ta kara a jere, ya haifar da koman baya a duniya baki daya, kuma 90% na masanan da aka tattauna da su, sun yi hasashen cewa, saboda da mataki na Amurka, ana fuskantar karin kalubalen hauhawar farashi.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Amurka ta samar da karin kudaden dala da nufin sassauta matsalar da ta fuskanta da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki a cikin gida, amma hakan bai kai ta ga samun nasara ba.

A maimakon haka ma, sai matakin ya haifar da hauhawar farashin kayayyaki da kara gibi tsakanin mawadata da talakawa. Ba yadda zai yi sai babban bankin Amurka ya kara kudin ruwa, idan ba haka ba, jama’a za su nuna adawa da gwamnati, da haddasa rashin tabbas a zamantakewar al’umma, kana rikici da koma baya a cikin gida zai tsananta matuka.

Amma, matakin da Amurka ke dauka ya shafi wasu kasashe marasa karfi, wadanda farfadowar tattalin arzikinsu ke da rauni, baya ga haddasa hasara da mummunan sakamakon da zai biyo ga irin wadannan kasashe.

‘Yan siyasar Amurka ba su yi la’akari da muradun jama’a da rikicin da sauran kasashe za su fuskanta ba, abin da ya dame su shi ne moriyar siyasa da ta sanya gaba. Kuma suna sane da cewa, duniya za ta dandana kudar matakan da suka dauka, kamar wannan karo da ta kara kudin ruwa. (Mai zane da rubuta:MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Birtaniya Ta Yi Shawarwari Kan Ikon Mallakar Tsibiran Malvinas

Next Post

Wata Tsaleliyar Budurwa A Indiya Ta Angonce Da Kare    

Related

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

4 minutes ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

1 hour ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

2 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

4 hours ago
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

1 day ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

1 day ago
Next Post
Wata Tsaleliyar Budurwa A Indiya Ta Angonce Da Kare    

Wata Tsaleliyar Budurwa A Indiya Ta Angonce Da Kare    

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.