• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 weeks ago
in Labarai
0
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin ‘Yan kwanakin nan al’ummar Jihar Kano musamman kwaryar birni na fama da matsalar faɗace faɗacen daba wanda a halin yanzu ke zama wata barazana ga zaman lafiyar jama’a.

A wannan karon lamarin na ɗaukar wani sabon salon ta yadda lamarin ya wuce tsakanin waɗanda ke faɗa da juna, a wasu lokutan tsakanin waccan unguwa da wancan, yanzu maharan sun fara kai irin wannan farmakin har cikin gidajen al’umma.

Wannan annoba ta faɗace faɗaɓen da kwacen wayoyi tafi ta azzara a yankunan Rijiyar Lemo, Dorayi, Sheka, Kofar mata Gwammaja da sauransu. Ko a ranar Alhamis da ta gabata al’ummar unguwannin Ƙofar Mata, Zage, Yakasai, Fagge da wasu unguwanni a cikin ƙwaryar birinin na Kano an wayi gari da irin wannan ta’asa, inda maharan suka afkawa unguwar Ƙofar Mata har zuwa ranar Juma”a ana wannan ɗauki badaɗin.

Suma al’ummar Sheka da ke makwabtaka da ƙwaryar birnin na Kano na fama da wannan babbar matsala, amma dai an samu wata gagarumar nasarar da ta kai ga damƙe babban gogarman waɗannan masu ta’annaci da ake kira Mu’azu Ɓarga, wannan matashi ya jima yana addabar wannan yankin dama unguwannin irin Medile, Shagari Kwatas, Sabuwar Gandu da sauransu.

Nasarar damƙe Ɓarga ta bayar damar samun bayannan abokansa da suke aikata wannan ɓarna, rundunar ‘yan sandan Kano sashin ‘Anty Daba’ ne suka dirarwa wannan shahararren gagararren ƙofar rago kuma aka damƙe shi, wanda yanzu haka yana hannun rundunar ‘yan sandan Kano yana taimakawa rundunar wajen damke waɗanda ya sanar da rundunar yadda suke aikata wannan ta’addanci tare.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Sakamakon kama Mu’azu Ɓarga, yanzu haka abokan ta’asar tasa sai tsallakewa suke domin tserewa kamun rundunar ‘yan sanda, duk da gudun da suke rundunar na ci gaba da farautarsu har kuma an samu nasarar ƙara damƙe mutane biyu cikin sama da mutane arba’in da Ɓarga ya bayyana wa ‘yan sanda. Wannan tasa a ranar Juma’ar da ta gabata Al’ummar Sheka ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Muryar Jama’ar Sheka ta ziyarci Shelkwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai domin jinjina wa ƙoƙarinsu.

Cikin shahararrun mafaɗatan da suka gamu da ajalinsu alokacin arangama daban-daban akwai matashin da ya addabi al’ummar Unguwar Ɗorayi mai Suna Barakita, sai kuma wani mai suna Khalufa ɗan unguwar Ƙofar Mazugal Da kuma wani guda da ke tafka irin wannan ta’asa a unguwar Gwammaja duk a kwaryar birnin Kano.

Yanzu haka dai a iya cewa faɗan daba da ƙwacen wayoyin gannu na neman zama ruwan dare a Jihar Kano, sai dai kuma rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ƙarƙashin Kwamiahinan da ke jagorantar operation ba sani ba sabo, ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan na Kano Abdullahi Haruna Kiyawa na ci gaba da samun nasarar kakkaɓe mafaɗatan tare da shiga lungu da saƙo domin farautar maɓarna

tan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dabakano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Next Post

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Related

2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

12 minutes ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

8 hours ago
Gwamna Yusuf
Labarai

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

9 hours ago
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya
Manyan Labarai

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

11 hours ago
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro
Labarai

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

12 hours ago
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano
Manyan Labarai

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

14 hours ago
Next Post
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

LABARAI MASU NASABA

2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

September 3, 2025
Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.