• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) da kungiyar raya mu’amala tsakanin daliban Amurka da Sin, sun kaddamar da bikin raya mu’amalar matasa da yaran Sin da Amurka mai taken “Zuwan Abokai Daga Nesa”, a jiya Litinin a nan birnin Beijing, wanda ya kasance wani bangare na mu’amala tsakanin matasan Amurka dubu 50 dake ziyara a Sin, da kuma takwarorinsu na kasar Sin.

Da farko, a matsayinta na kafar yada labarai, CMG ba ta tsaya ga bayar da labaran kadai ba, ta zo da wani sabon salon, inda ta kasance gada tsakanin Sin da sauran sassan duniya, ta hanyar wayar da kan jama’a game da kasar Sin da kuma yayata kyawawan manufofi da dabi’u da al’adun kasar, domin su isa ga al’ummun duniya, har su kara fahimtar kasar Sin, sabanin labaran da suka saba ji daga kafafen yada labarai na yammacin duniya.

  • An Yi Bikin Mu’Amalar Matasa Da Yaran Sin Da Amurka A Birnin Beijing
  • Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Hakika, yadda ake samun tankiya da kalamai na rashin fahimta daga ’yan siyasar Amurka, na matukar bukatar karin fahimta da wayewar kai domin hakan ba hanya ce mai bullewa ga dangantaka tsakanin manyan kasashen ba.

Shirya tarukan inganta mu’amala da cudanya tsakanin yara da matasa irin wannan, zai bayar da  gagarumar gudunmawa wajen kyautata fahimta da alaka tsakanin zuri’o’i masu tasowa na Sin da Amurka. Kamar yadda bahaushe kan ce, “yara manyan gobe”, idan aka fara samun kyakkyawar fahimta da mu’amala tsakanin matasa da yara tun daga yanzu, to a nan gaba bangarorin biyu za su kasance aminai kuma ’yan uwa, wadanda suka san juna, suka kuma san bambance-bambacen dake akwai tsakanin al’adu da dabi’unsu, kuma suka lalubo yadda za a yi zaman jituwa da girmama juna a tsakaninsu.

A baya bayan nan, an ga yadda dalibai da malamai na makarantar sakandare ta Lincoln ta Amurka suka aikowa shugaba Xi Jinping da Uwargidansa katin gaisuwar sabuwar shekara, inda shugaban da uwargidansa suka mayar musu da amsa, har ma da gayyatarsu zuwa kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Gani ya kori ji. Gayyatar karin matasan Amurka zuwa kasar Sin, ya nuna cewa, kofar Sin a bude take, tana maraba da baki, haka kuma ba ta da wani abun boyewa. Ya kuma kara nuna kaifin basirar Sin na hangen nesa da sanin ya kamata, a kokarinta na raya dangantakarta da Amurka ta yadda makomarta za ta kasance mai haske. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Mutane 58 Kan Zargin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane A Adamawa

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

31 minutes ago
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

2 hours ago
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

3 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

5 hours ago
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

23 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

24 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 45 Kan Laifuka Daban-daban A Adamawa

'Yansanda Sun Kama Mutane 58 Kan Zargin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.