• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) da kungiyar raya mu’amala tsakanin daliban Amurka da Sin, sun kaddamar da bikin raya mu’amalar matasa da yaran Sin da Amurka mai taken “Zuwan Abokai Daga Nesa”, a jiya Litinin a nan birnin Beijing, wanda ya kasance wani bangare na mu’amala tsakanin matasan Amurka dubu 50 dake ziyara a Sin, da kuma takwarorinsu na kasar Sin.

Da farko, a matsayinta na kafar yada labarai, CMG ba ta tsaya ga bayar da labaran kadai ba, ta zo da wani sabon salon, inda ta kasance gada tsakanin Sin da sauran sassan duniya, ta hanyar wayar da kan jama’a game da kasar Sin da kuma yayata kyawawan manufofi da dabi’u da al’adun kasar, domin su isa ga al’ummun duniya, har su kara fahimtar kasar Sin, sabanin labaran da suka saba ji daga kafafen yada labarai na yammacin duniya.

  • An Yi Bikin Mu’Amalar Matasa Da Yaran Sin Da Amurka A Birnin Beijing
  • Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Hakika, yadda ake samun tankiya da kalamai na rashin fahimta daga ’yan siyasar Amurka, na matukar bukatar karin fahimta da wayewar kai domin hakan ba hanya ce mai bullewa ga dangantaka tsakanin manyan kasashen ba.

Shirya tarukan inganta mu’amala da cudanya tsakanin yara da matasa irin wannan, zai bayar da  gagarumar gudunmawa wajen kyautata fahimta da alaka tsakanin zuri’o’i masu tasowa na Sin da Amurka. Kamar yadda bahaushe kan ce, “yara manyan gobe”, idan aka fara samun kyakkyawar fahimta da mu’amala tsakanin matasa da yara tun daga yanzu, to a nan gaba bangarorin biyu za su kasance aminai kuma ’yan uwa, wadanda suka san juna, suka kuma san bambance-bambacen dake akwai tsakanin al’adu da dabi’unsu, kuma suka lalubo yadda za a yi zaman jituwa da girmama juna a tsakaninsu.

A baya bayan nan, an ga yadda dalibai da malamai na makarantar sakandare ta Lincoln ta Amurka suka aikowa shugaba Xi Jinping da Uwargidansa katin gaisuwar sabuwar shekara, inda shugaban da uwargidansa suka mayar musu da amsa, har ma da gayyatarsu zuwa kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Gani ya kori ji. Gayyatar karin matasan Amurka zuwa kasar Sin, ya nuna cewa, kofar Sin a bude take, tana maraba da baki, haka kuma ba ta da wani abun boyewa. Ya kuma kara nuna kaifin basirar Sin na hangen nesa da sanin ya kamata, a kokarinta na raya dangantakarta da Amurka ta yadda makomarta za ta kasance mai haske. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Mutane 58 Kan Zargin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane A Adamawa

Related

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

45 minutes ago
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici
Daga Birnin Sin

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

4 hours ago
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

5 hours ago
Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa
Daga Birnin Sin

Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa

15 hours ago
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
Daga Birnin Sin

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

22 hours ago
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
Daga Birnin Sin

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

23 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 45 Kan Laifuka Daban-daban A Adamawa

'Yansanda Sun Kama Mutane 58 Kan Zargin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

May 31, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

May 31, 2025
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

May 31, 2025
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

May 31, 2025
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.