• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) da kungiyar raya mu’amala tsakanin daliban Amurka da Sin, sun kaddamar da bikin raya mu’amalar matasa da yaran Sin da Amurka mai taken “Zuwan Abokai Daga Nesa”, a jiya Litinin a nan birnin Beijing, wanda ya kasance wani bangare na mu’amala tsakanin matasan Amurka dubu 50 dake ziyara a Sin, da kuma takwarorinsu na kasar Sin.

Da farko, a matsayinta na kafar yada labarai, CMG ba ta tsaya ga bayar da labaran kadai ba, ta zo da wani sabon salon, inda ta kasance gada tsakanin Sin da sauran sassan duniya, ta hanyar wayar da kan jama’a game da kasar Sin da kuma yayata kyawawan manufofi da dabi’u da al’adun kasar, domin su isa ga al’ummun duniya, har su kara fahimtar kasar Sin, sabanin labaran da suka saba ji daga kafafen yada labarai na yammacin duniya.

  • An Yi Bikin Mu’Amalar Matasa Da Yaran Sin Da Amurka A Birnin Beijing
  • Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Hakika, yadda ake samun tankiya da kalamai na rashin fahimta daga ’yan siyasar Amurka, na matukar bukatar karin fahimta da wayewar kai domin hakan ba hanya ce mai bullewa ga dangantaka tsakanin manyan kasashen ba.

Shirya tarukan inganta mu’amala da cudanya tsakanin yara da matasa irin wannan, zai bayar da  gagarumar gudunmawa wajen kyautata fahimta da alaka tsakanin zuri’o’i masu tasowa na Sin da Amurka. Kamar yadda bahaushe kan ce, “yara manyan gobe”, idan aka fara samun kyakkyawar fahimta da mu’amala tsakanin matasa da yara tun daga yanzu, to a nan gaba bangarorin biyu za su kasance aminai kuma ’yan uwa, wadanda suka san juna, suka kuma san bambance-bambacen dake akwai tsakanin al’adu da dabi’unsu, kuma suka lalubo yadda za a yi zaman jituwa da girmama juna a tsakaninsu.

A baya bayan nan, an ga yadda dalibai da malamai na makarantar sakandare ta Lincoln ta Amurka suka aikowa shugaba Xi Jinping da Uwargidansa katin gaisuwar sabuwar shekara, inda shugaban da uwargidansa suka mayar musu da amsa, har ma da gayyatarsu zuwa kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Gani ya kori ji. Gayyatar karin matasan Amurka zuwa kasar Sin, ya nuna cewa, kofar Sin a bude take, tana maraba da baki, haka kuma ba ta da wani abun boyewa. Ya kuma kara nuna kaifin basirar Sin na hangen nesa da sanin ya kamata, a kokarinta na raya dangantakarta da Amurka ta yadda makomarta za ta kasance mai haske. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
Daga Birnin Sin

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
Daga Birnin Sin

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 45 Kan Laifuka Daban-daban A Adamawa

'Yansanda Sun Kama Mutane 58 Kan Zargin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.