• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjojin Farko Da Ba Sa Bukatar Bin Tsauraran Matakan Yaki Da COVID-19 Sun Sauka A Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Da safiyar Lahadin nan ne, jiragen sama dauke da fasinjoji na farko da ba sa bukatar bin tsauraran matakan yaki da annobar COVID-19 suka sauka, a filayen jiragen saman biranen Guangzhou da Shenzhen dake lardin Guangdong na kudancin kasar Sin. 

Hukumar Kwastam ta kasar ta ce jiragen saman 2, dauke da fasinjoji 387, sun taso ne daga birnin Toronto da kasar Singapore, sun kuma sauka yau Lahadi, ranar da kasar Sin ke kawo karshen aiwatar da tsauraran matakan shige da ficen fasinjoji sakamakon bazuwar cutar COVID-19.

  • Jami’an Diflomasiyyar Kasashen Waje Dake Sin Sun Yaba Da Matakan Yaki Da COVID-19 Da Kasar Ta Aiwatar

A cewar babban daraktan hukumar Yu Jianhua, matakan kandagarki da yaki da cutar COVID-19 na Sin, sun yi matukar inganta, kuma wajibi ne a aiwatar da su, tare da daidaita ayyukan kwastam sannu a hankali cikin tsari.

A wani ci gaban kuma, a dai yau Lahadin, yankin musamman na Hong Kong, ya bude damar zirga-zirgar fasinjoji tsakanin sa da babban yankin kasar Sin. A lokaci guda kuma, al’umma sun fara tafiye tafiye tsakanin yankunan kan iyakar kasar ta Sin.

A watan Disamban da ya gabata ne kasar Sin ta sanar da dage tsauraran matakan yaki da COVID-19, wadanda suke bukatar matafiya daga kasashen waje dake shigowa kasar yin gwajin kwayoyin cutar COVID-19, tare da bukatar su da su killace kan su tsawon wasu kwanaki.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

A yanzu, fasinjoji masu shigowa kasar na bukatar nuna shaidar gwaji ta tsawon sa’o’i 48 ne kawai kafin hawowa jirgi zuwa kasar, kuma ba bu bukatar neman takardar shaidar musamman ta ingancin lafiya, daga ofisoshin jakadancin Sin dake kasashen waje kafin shigowa kasar. (Saminu Alhassan)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira
Daga Birnin Sin

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Next Post
Wani Matashi Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa Da ‘Yarta A Kano

Wani Matashi Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa Da 'Yarta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.