• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

by Khalid Idris Doya
12 months ago
Matasa

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya nuna takaicinsa kan yadda hazikan matasan Nijeriya ke sulalewa su na ficewa daga cikin kasar zuwa kasashen ketare.

A cewar Jega, a irin wannan yanayin na tafiya zuwa wasu wurare domin gwagwarmayar neman rayuwa mai kyau, babban barazana ce ga fatan ci gaban kasar nan.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

Da yake magana a wajen kaddamar da wata kungiya mai zaman kanta, mai rajin farfado da Nijeriya (URNI) a Abuja, Jega ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi duk mai yiwuwa wajen farfado da fatan ci gaban kasar nan.

Ya ce, “Yanayin gwagwarmayar kasar nan a halin yanzu, wanda ya kunshi har da yanayin talauci da ke addamar kasar da kuma karuwar ficewar matasa masu hazaka da aka fi sani da ‘Japa’ abun damuwa ne matuka gaya.

“Wannan yanayin babban barazana ce ga fatan ci gaba, dole ne masu kishin kasa su tashi tsaye wajen yin duk mai yiwuwa domin farfado da fata ga cikin kasar.”

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Yayin da yake cewa lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kai, lokaci ne da kasar ta zama fitilar bege ga dukkanin Afrika, wanda ya zaburar da al’ummomin da suka kasance bakaken fata a fadin duniya.

Jega ya jinjina wa shugabannin da suka sadaukar da kansu a jamhuriyya ta farko har aka samu nasarar da aka samu.

Ya kara da cewa, wadannan shugabannin masu kishi su ne suka aza tubalin ci gaban kasar nan da har yanzu ake kan mora.

Tsohon shugaban INEC ya nemi ‘yan Nijeriya da su shure kowace irin ikirari da ke nuni da cewa Nijeriya kasa mara ci gaba. Sai dai, ya nemi da a yi aiki tukuru domin gina kasa da cire kowace irin bambance-bambance domin al’umman kasar nan su more kasar.

A nasa jawabin, ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya ce, ‘yan Nijeriya sun cancanji rayuwa mai inganci fiye da a zauna a yi ta musu karin alkawura.

Ministan wanda ya samun wakilcin darakta janar na hukumar wayar da kai ta kasa, Lanre Isa Onilu, ya ce akwai bukatar alkawuran da aka yi wa ‘yan Nijeriya an cika su. Ya ce, “Domin tabbatar da azamarmu, dole ne mu tabbatar mun aiwatar da alkawuran da muka yi wa jama’anmu.”

Uban kungiyar URNI, Hassan Tukur, ya ce, matsalolin da suke akwai suna da nasaba da rashin shugabanci na kwarai, ya nemi a cire bambancin addini ko na kabilanci domin ganin rayuwa da kyautata da ingantuwa a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal
Labarai

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci
Labarai

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Next Post
Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote

Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai - Matatar Dangote

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.