• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

by Naziru Adam Ibrahim
10 months ago
Kano

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya zargi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ƙara ta’azzara matsala ga al’ummar a jihar Kano, ta hanyar yin watsi da biyan sama da Naira biliyan 48 na haƙoƙin ‘yan fansho a tsawon shekaru takwas da ya yi yana mulki.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kaso na uku na biyan bashin Naira biliyan 5 na kuɗaɗen alawus-alawus ga waɗanda suka yi ritaya a ranar Alhamis, a gidan gwamnati Gwamna Yusuf, ya nuna matukar damuwarsa kan halin da ‘yan fanshon jihar ke ciki.

  • Gwamna Yusuf Ya Gargaɗi Kwamishinoninsa Kan Duk Wani Yunƙurin Kawo Rarrabuwar Kai A Majalisar Zartarwar Kano 
  • Za a Fara Kera Motoci Da Babura Masu Amfani Da Lantarki A Kano

Gwamna Yusuf, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar ya bayyana cewa jimillar kuɗaɗen tallafin da aka ware sun haura sama da Naira biliyan 48, lamarin da ya bayyana a matsayin babbar barazana ga zaman ci gaban da Kano, ta taba fuskanta tun bayan ƙirƙiro ta a shekarar 1967.

Gwamna Yusuf, ya bayyana cewa, domin rage raɗaɗin ’yan fanshon, gwamnatinsa ta raba Naira biliyan 16 ga ma’aikata 6,886 da suka yi ritaya, wanda hakan na daga cika alƙawarin da ya ɗauka lokacin yakin neman zabe na tallafa wa tsofaffin da suka yi wa jihar hidima, kana ya kuma umurci hukumar fansho na jihar da ta zakulo waɗanda suka rasa rayukansu domin biyan magadansu Naira miliyan 846 da ke adane.

Gwamna Yusuf ya kuma bayyana amincewa da ƙara mafi ƙarancin haƙƙin ‘yan fansho daga Naira 5,000 zuwa Naira 20,000 duba da yanayin rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da kuma tsadar rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Karɓi Ƙarin $52.88m Da Aka Kwato Daga Hannun Diezani

Nijeriya Ta Karɓi Ƙarin $52.88m Da Aka Kwato Daga Hannun Diezani

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.