• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

by Naziru Adam Ibrahim
10 months ago
Kano

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya zargi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ƙara ta’azzara matsala ga al’ummar a jihar Kano, ta hanyar yin watsi da biyan sama da Naira biliyan 48 na haƙoƙin ‘yan fansho a tsawon shekaru takwas da ya yi yana mulki.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kaso na uku na biyan bashin Naira biliyan 5 na kuɗaɗen alawus-alawus ga waɗanda suka yi ritaya a ranar Alhamis, a gidan gwamnati Gwamna Yusuf, ya nuna matukar damuwarsa kan halin da ‘yan fanshon jihar ke ciki.

  • Gwamna Yusuf Ya Gargaɗi Kwamishinoninsa Kan Duk Wani Yunƙurin Kawo Rarrabuwar Kai A Majalisar Zartarwar Kano 
  • Za a Fara Kera Motoci Da Babura Masu Amfani Da Lantarki A Kano

Gwamna Yusuf, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar ya bayyana cewa jimillar kuɗaɗen tallafin da aka ware sun haura sama da Naira biliyan 48, lamarin da ya bayyana a matsayin babbar barazana ga zaman ci gaban da Kano, ta taba fuskanta tun bayan ƙirƙiro ta a shekarar 1967.

Gwamna Yusuf, ya bayyana cewa, domin rage raɗaɗin ’yan fanshon, gwamnatinsa ta raba Naira biliyan 16 ga ma’aikata 6,886 da suka yi ritaya, wanda hakan na daga cika alƙawarin da ya ɗauka lokacin yakin neman zabe na tallafa wa tsofaffin da suka yi wa jihar hidima, kana ya kuma umurci hukumar fansho na jihar da ta zakulo waɗanda suka rasa rayukansu domin biyan magadansu Naira miliyan 846 da ke adane.

Gwamna Yusuf ya kuma bayyana amincewa da ƙara mafi ƙarancin haƙƙin ‘yan fansho daga Naira 5,000 zuwa Naira 20,000 duba da yanayin rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da kuma tsadar rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu
Manyan Labarai

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Karɓi Ƙarin $52.88m Da Aka Kwato Daga Hannun Diezani

Nijeriya Ta Karɓi Ƙarin $52.88m Da Aka Kwato Daga Hannun Diezani

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.