• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gasar Cin Kofin Turai 2024: Kasashe Na Ci Gaba Da Shirye-Shirye

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Gasar Cin Kofin Turai 2024: Kasashe Na Ci Gaba Da Shirye-Shirye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu kasashe 20 ne suka samu gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Turai na Euro 22024 kai tsaye, wanda Kasar Jamus za ta karbi bakuncin wasannin a shekara mai zuwa ta 2024.

Kasar Ingila, wadda Gareth Southgate ke jan ragama tana cikin tawagogin da za su jira raba jadawali, bayan da ta ja ragamar rukuni na uku, itama Scotland ta samu gurbi na zuwa gasar.

  • Shirin Rage Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi Daga Afrilun 2024 – Minista
  • Masani: Zamanantarwa Irin Ta Sinawa Wani Sabon Salo Ne Na Wayewa

Dukkan wadda ta yi ta daya da ta biyu a kowanne rukuni, su ne suka samu tikiti kai tsaye a wasannin da za a fara daga watan Yuni zuwa Yulin na shekarar ta 2024 kamar yadda yake a doka.

Yanzu kenan saura gurbi uku ya rage, inda kasashe 12 za su buga wasannin cike gurbin shiga Euro 2024 domin samun kasashen da za su cike gurbin gasar da ake ganin za ta kayatar matuka.

Tawaga nawa ce za ta buga Euro 2024?

Labarai Masu Nasaba

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Kasa 23 ce za ta barje gumi a Euro 2024, inda Jamus da za ta karbi bakuncin wasannin ce kadai da ta samu takiti kai tsaye saboda a doka duk kasar da za ta karbi bakunci tana da tikiti kyauta.

A ranar Talatar watan da ya gabata aka kammala karawar cikin rukuni ta yadda aka samu kasashe 20 da suka kai Euro 2024 kai tsaye kuma su ne za su fafata tare da ragowar kasashe ukun da za su bi su nan gaba.

Kawo yanzu kasashen da suka samu gurbin shiga gasar sun hada da kasashen Sipaniya, Scotland, France, Netherlands, England, Italy, Turkey, Croatia, Albania, Jamhuriyar Czech, Belgium, Austria, Hungary, Serbia, Denmark, Slobenia, Romania, Switzerland, Portugal da kuma Slobakia.

Yanzu kasa uku za a tantance, bayan buga karawar cike gurbi, domin samun 24 da za su fafata a Jamus a 2024 kuma za a raba jadawalin cike gurbi bisa la’akari da kwazon tawaga a wasannin da suka buga a cikin rukuni.

Bayan raba jadawalin, kasar Wales za ta karbi bakuncin Filland a wasan cike gurbi na gasar Euro 2023 da Jamus za ta karbi bakunci sannan kasar da ta yi nasara cikinsu za ta buga wasan gaba da Poland ko Estonia a gida domin samun gurbi a gasar da za a fara a ranar 14 ga watan Yuni a kare a ranar 14 ga watan Yuli 2024.

A rukuni na biyu akwai wasa tsakanin Isra’ila da Iceland, yayin da Bosnia Herzogobina za ta karbi bakuncin Ukraine, sannan a rukuni na uku Georgia da Ludembourg ne za su fatata waca ta yi nasara kuma za ta barje gumi da Kazakhstan ko kuma Greece.

Yadda Aka Raba Jadawalin:

Rukunin (A) Poland da Estonia – Wales da Finland. Rukunin (B) Israel da Iceland.

Bosnia-Herzegobina da Ukraine. Rukunin (C) Georgia da Ludembourg Greece da Kazakhstan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Guterres: Wajibi Ne Shugabannin Duniya Su Kawo Karshen Mummunan Dumamar Yanayi

Next Post

An Kammala Wasan  Karshen Damben Warriors  Na Wannan Shekarar A Kano

Related

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

8 hours ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

1 day ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

3 days ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

3 days ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

5 days ago
Next Post
An Kammala Wasan  Karshen Damben Warriors  Na Wannan Shekarar A Kano

An Kammala Wasan  Karshen Damben Warriors  Na Wannan Shekarar A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.