• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiyar Lamari Kan Duwatsun Kasar Kongo Masu Dauke Da Lantarki

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Kasar kongo

Miliyoyin mutane a ciki da wajen nahiyar Afirka sun kalli wasu bidiyoyi da ke nuna yadda wasu duwatsu ke samar da lantarki.

Daya daga cikin bidiyoyin ya nuna yadda wutar ke tartsasti yayin da aka hada duwatsun biyu, inda aka rubuta kalaman da ke cewa ”An samu duwatsun lantarki a Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo”.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Gina Budadden Tsarin Raya Tattalin Arzikin Duniya

Wannan bidiyo ya yadu kamar wutar daji a lokacin da hamshakin kan kasuwar Afirkan nan Daniel Marben ya wallafa shi a shafinsa mai mabiya dubu 800 tare da rubuta Kalaman: ”Karin matsaloli na tunkaro mu, ina tausaya wa nahiyata Afirka”
Wani mai amfani da shafin Tuwita, ya yi tsokaci a kan bidiyon da Marben ya wallafa, ta hanyar wallafa wani bidiyo da ke nuna wani mutum rike da kwan lantarki kaure da wayoyi guda biyu inda kwan lantarkin ke kawo hasken wuta da zarar ya jona wayoyin a jikin wani karamin dutse da ke hannunsa.

Sa’o’i bayan nan ne kuma Marben ya sake wallafa wannan bidiyo a shafin nasa, inda fiye da mutum miliyan kaya suka kalle shi.
Fitaccen shafin Tuwitan nan mai suna ‘Africa Archibes’ ya sake wallafa duka bidiyoyin biyu, inda kaya daga cikin bidiyoyin aka kalle shi sau kusan miliyan 35.

To sai dai babu tabbas game gaskiyar lamarin duwatsun.

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Bincike ya nuna cewa bidiyon farko da Marben ya wallafa, an fara wallafa shi a shafin Facebook na Jami’ar Mohamed na kaya, da ke Oujda a Morocco.

Inda aka rubuta kalmar ”Lithium!!?” ba tare da karin bayani ba.
BBC ta tuntubi Jami’ar, to sai dai har yanzu babu martani daga gare ta.

To amma abu mafi muhimmanci shi ne shin da gaske ne duwatsun da aka nuna a bidiyon za su iya rike ko samar da lantarki?

Dakta Ikenna Okonkwa malami a sashen koyar da ilimin ma’adinai na jami’ar Nijeriya ya ce ”ba zai yiwu ba”.
Ya ce “Duwatsun sun yi kama da ma’adinin zinc ko dalma, don haka ba su da karfin ma’adinin da zai samar da lantarki”.

Za su iya rike wutar da ire-iren ma’adinai irinsa ke da ita, to amma ba ta da karfin da za ta haska kwan lantarki”, in ji Dakta Okonkwo.

Don haka a ganinsa wannan bidiyo kawai wani ”siddabaru ne”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Firaministan Kambodiya: Takunkuman Da Ake Sanyawa Babu Tsayawa Na Haifar Da Tashe-Tashen Hankali A Duniya

Firaministan Kambodiya: Takunkuman Da Ake Sanyawa Babu Tsayawa Na Haifar Da Tashe-Tashen Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.