ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gbemisola Yusuf: Daga Sayar Da Ruwa A Filin Wasa Na Agege Zuwa Alkaliyar Wasa

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 year ago
Gbemisola

Matashiya Gbemisola Yusuf mace ce mai hankoron jan ragamar rayuwarta da kanta domin tun tana shekara 21 da haihuwa ta fara alkalancin wasa a Nijeriya inda ta jagoranci wasanni 22 a filin wasa na Maracana da ke Legas.

 

Matakin da take kai a yanzu ba karamin abin alfahari ba ne saboda tana cikin alkalan wasa mata kalilan a Nijeriya duk da cewa an samu karuwar alkalan wasa mata a Afirka a ‘yan shekarun nan, har yanzu mata ba su da yawa a harkar alkalancin wasa a Afirka da duniya baki daya.

ADVERTISEMENT
  • Aikin Matatar Mai Na Ya Hana Ni Sayen Arsenal A 2020 – Dangote
  • Ba Kare Bin Damo Tsakanin Man City Da Arsenal A Etihad 

Zuwa shekara ta 2023, mata 53 ne kawai ke cikin alkalan wasa na hukumar kwallon kafa ta duniya, kuma sun kunshi mataimaka alkalin wasa, da alkalan wasan kwallon dabe (Futsal), amma hakan ma an samu karuwa duk da haka idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

Afirka ta Kudu da Moroko ne suka fi yawan alkalan wasa mata da ke busa wasanni a babban mataki duk da cewa alkalan wasa mata kan fuskanci kalubale mai yawa a Nijeriya da Afirka saboda al’adu da addinai, sai dai da ma can al’adu kan hana mata shiga wasanni musamman ma kwallon kafa.

 

Gbemisola Yusuf, wadda aka haifa a yankin Agege na Jihar Legas, filin wasan da ke yankin muhimmin abu ne a rayuwarta da ma danginta domin lokacin da take yarinya, takan je filin wasan tare da mahaifiyarta suna sayar da ruwa da lemo ga ‘yanwasa, da masu koyarwa, da ma ‘yankallo kuma a wannan lokacin ne sha’awar kwallon kafa ta shiga rayuwarta.

 

Bayan ta fara a matsayin ‘yar wasa, Gbemisola ta koma akalancin wasa domin wani mai gidanta mai suna Dele Atoun, tsohon alkalin wasa kuma sakataren majalisar alkalan wasa ta Legas, kan tuna lokacin da ta fara wasa.

 

Ya ce ta gina kwarin gwiwa a ranta duk da yadda take ganin ana kai wa alkalan wasa hari, ana jifan su, amma kuma ta ga yadda suka yi nasara kuma hakan ya kara wa mata kwarin gwiwa domin nan gaba ma wasu su fito.

 

Gbemisola ta fara alkalancin wasa lokacin da take shekara 14 da haihuwa bayan ta shiga wani shiri da hukumar kwallon kafar Afirka CAFN ta shirya domin zakulowa da kuma ba da horo ga matasa a alkalancin wasa.

 

Sai dai hanyar da ta bi ba mai sauki ba ce musamman a Nijeriya, saboda cin zarafi ta hanyar kalamai da ma yadda magoya baya kan kai wa alkalan wasa da ‘yanwasan hari amma duk da haka ta jure har ta cika burinta.

 

Wani bincike da kungiyar alkalan wasa ta Nijeriya NRA ta gudanar ya nuna cewa kashi 80 cikin 100 na mutanen da suka ba da amsa sun ce sun fuskanci wani nau’i na cin zarafi a lokacin da suke alkalancin wasa.

 

Itama Gbemisola ta fuskanci irin wannan yanayin amma kuma hakan bai sanyaya mata gwiwa ba inda ta ce alkalancin wasa ne aiki mafi wahala a duniya domin za ka yanke hukunci a cikin ‘yan dakikoki, ko da kuwa ka yi daidai ko akasin haka. Muhimmiyar damar da Gbemisola ta samu ita ce, lokacin wani wasa a Legas tana ‘yar shekara 18. Alkalan wasan ba su zo ba, ‘yan mintuna kafin lokacin take wasan, sai aka nemi Gbemisola da ke taimaka wa mahaifiyarta sayar da ruwa a filin wasan ta jagoranci wasan kuma kusan ta yi komai daidai a wasan, kuma hakan ya ja hankalin mutane da yawa.

 

Daga nan ne kuma Gbemisola ta daukaka, inda har ta yi busa a gasar Firimiyar Nijeriya ta mata amma kuma kai wa wannan mataki ma na da nasa kalubalen, musamman ga mata domin hari kan alkalan wasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, kuma ya kan hada da zagi da ma kai hari.

 

A 2021, wasu ‘yankallo sun kori wata alkaliyar wasa yayin wani wasan hamayya, lamarin da ya jawo tir daga hukumar kwallon kafa ta Nijeriya da kuma kiraye-kirayen tsaurara tsaro yayin wasanni musamman kan mata alkalan wasa.

 

Tun daga 2023, babu wata gasa a Nijeriya da ta fara amfani da na’urar BAR mai taimaka wa alkalin wasa, kuma hakan ya sa alkalan wasan Nijeriya ba su iya busa wasanni a wasannin duniya saboda ba su iya amfani da na’urar ba.

 

Gbemisola ta ce idan har ta dage da kokari a aikinta, ba ta da wata fargaba domin kuwa ta kan yi bakin kokarinta kawai ta bar wa Allah sauran domin a alkalancin wasa ba komai za ka yi daidai ba kuma ba zaka taba farantawa kowa rai ba.

 

A rayuwar Gbemisola, filin wasa na Agege ba wuri ba ne kawai, wata alama ce ta mafarin sana’arta domin duk da cewa yanzu ta daina sayar da ruwa saboda Jami’ar Legas da take zuwa karatu, ba ta manta da wannan lokaci ba.

 

“Komai na rayuwata ya ta’allaka ne da filin wasa na Agege domin a nan na samu kwarin gwiwar shiga aikin alkalancin wasa, kuma yankin gaba dayansa ya taimaka min sosai.”

 

A lokacin da take hira da manema labarai.

Gbemisola na cikin alkalan wasan da suka busa gasar makarantu ta Afirka, inda ta shiga wasannin neman gurbi da kuma gasar kanta a Tanzania domin a cewarta, burinta ne ya cika kuma ta ji dadin yin hakan, kamar yadda ta bayyana.

 

Ta ci gaba da cewa “Zuwa kasashe da kuma tattaunawa da alkalai daban-daban, da kuma koyon harsuna abubuwa ne da suka taimaka mata domin iya magana da harsuna daban-daban kan taimaka wa alkalin wasa wajen karfafa ikonsa a cikin fili.

 

Ta kara da cewa abu ne mai muhimmanci sosai saboda ba ta taba tsammanin za ta hadu da mutanen da ta gani ba kuma shi ma mai gidanta Atou ya ce yana alfahari da nasarorinta domin labarinta mai karfafa gwiwa ne da jajircewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey
Wasanni

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

December 20, 2025
FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

December 17, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta'adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.