• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Dangote Ta Bai Wa Jihar Bauchi Tallafin Buhun shinkafa 25,000

by Sulaiman
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Gidauniyar Dangote Ta Bai Wa Jihar Bauchi Tallafin Buhun shinkafa 25,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidauniyar Aliko Dangote ta bayar da tallafin buhunan shinkafa guda dubu ashirin da biyar (25,000) mai nauyin kilogiram 10 da aka rabar wa al’umma a ƙananan hukumomi 20 na jihar Bauchi da masallatai da cocina.

 

Babban manajan sashin kamfanonin Dangote, Ahmed Hashim ne ya miƙa buhunan shinkafar a madadin gidauniyar ga gwamnatin jihar Bauchi, inda aka rabar da shi a ranar Talata ga mabuƙata, ya shaida cewar a shekarar da ta gabata ma gidauniyar ta yi irin wannan rabon a faɗin ƙasar nan.

  • Sin Na Adawa Da Haramta Amfani Da DeepSeek Da Gwamnatin Amurka Ta Yi
  • Trump Zai Tattauna Da Putin Kan Kawo Ƙarshen Yaƙin Ukraine

Hashim, ya ce, “A kowace shekara cikin wata Ramadana mai albarka, muna ƙoƙarin tallafawa da kayan abinci ga marasa galihu da marasa ƙarfi a cikin al’umma ta hannun gidauniyar Dangote.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

“Wannan shi ne karo na biyu, a shekarar da ta gabata dukkanin ƙananan hukumomi a Nijeriya ta hannun jihohinsu sun samu tallafin buhun shinkafa miliyan ɗaya mai nauyin kilogiram 10. Don haka, a wannan shekarar ma muna sake yin makamancin na bara.”

 

Hashim ya yi tilawar cewa gidauniyar Dangote ta himmatu wajen samar da tallafin kayan abinci ga mabuƙata, tallafi a ɓangaren kiwon lafiya, gina ɗakunan kwanan ɗalibai a jami’o’i, da sauran tallafi ciki har da wanda gidauniyar ta yi a lokacin annobar Korona.

 

Ya ce tallafin dafawa ne kan ƙoƙarin da gwamnatocin jihohi ke yi wa al’ummarsu, ya yi fatan cewa shinkafar da suka kawo Bauchi ɗin za ta je kai tsaye ga waɗanda aka bayar domin su wato marasa ƙarfi da marasa galihu a cikin al’umma.

 

Da ta ke amsar tallafin haɗi da ƙaddamar da rabarwa, Kwamishiniyar ma’aikatar kula da harkokin jin ƙai ta jihar, Hon. Hajara Yakubu Wanka ta nuna matuƙar godiyarsu ga gidauniyar Dangote bisa ga wannan tallafin.

 

Ta ce, a daidai lokacin da suke ƙoƙarin kammala rabon tallafin azumin da gwamnan jihar Bala Muhammad ke yi ne suka samu wannan tallafin daga wajen Dangote, don haka ne ta ce hakan zai ƙara kyautata jin daɗin jama’a a irin wannan watan da jama’a ke fama da azumi.

 

A cewar ta, cikin adadin buhu 25,000 da gidauniyar ta kawo Bauchi, za a rabar da guda 500 ga kowace ƙaramar hukuma daga cikin su 20, sai kuma guda dubu 10 da aka ware domin rabarwa a masallatai da cocina, gami da sauran guda 5,000 da za a rabar ga sauran masu ruwa da tsaki.

 

Shi ma a jawabinsa a madadin ƙananan hukumomin jihar Bauchi kuma shugaban ALGON na jihar, Hon. Mahmood Baba Ma’aji ya fara ne da gode wa gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad a bisa tallafin da ya rabar ga ƙananan hukumomin jihar.

 

Hon. Ma’aji ya ce a satukan da suka wuce ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon tallafin azumin wanda kowace ƙaramar hukuma sai da ta ci gajiyar hakan.

 

A gefe guda, ya gode wa gidauniyar Dangote bisa ƙara samar da tallafi a jihar ya bada tabbacin cewa za su sanya ido wajen rabon kayan tare da tabbatar da cewa a waɗanda suka dace su ci gajiyar tallafin ne suka amfana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Haramta Amfani Da DeepSeek Da Gwamnatin Amurka Ta Yi

Next Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya

Related

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

3 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

16 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

21 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

23 hours ago
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.